fidelitybank

Ba za mu koma kungiyar ECOWAS ba – Nijar da Mali tare da Burkina Faso

Date:

Shugabannin gwamnatin mulkin soji a Nijar da Mali da kuma Burkina Faso sun ce ba zasu koma ƙungiyar bunƙasa tattalin arzikin yammacin Afirka, Ecowas ba.

Shugabannin uku sun gana a karon farko, domin ƙulla wata haɗaka da za ta fuskanci ƙalubalen da suke fuskanta daga ƙasashe maƙwabtan su.

A tsakanin 2020 zuwa 2023 sojoji suka ƙwace mulki a Mali da Burkina Faso da kuma Nijar, a wata guguwar juyin mulki da yankin ya yi fama da ita.

Dukkan ƙasashen uku da ke ƙarƙashin ƙawancen na Alliance of Sahel States suna fama da rikicin ƙungiyoyi masu iƙirarin jihadi, wanda kuma yana daga cikin dalilan da sojojin suka ce sun tilasta masu ƙwace mulki.

Da yake jawabi a wajen taron ƙasashen uku a Nijar, shugaban mulkin sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya ce ƙasashen sun yanke shawarar kafa wata haɗaka da za ta kula da muradun jama’arsu, ba tare da shisshigin ƙasashen waje ba.

”Za mu samar da gamayya ta zaman lafiya da taimakon juna da kuma kawo ci gaba a bisa mutumta al’adunmu na Afirka.” Inji Jana Tchiani.

A cikin watan Janairu ƙasashen suka sanar da shirin su na ficewa daga Ecowas, wadda itama za ta gudanar da taron ta a ranar Lahadi.

Janar Tchiani ya yi jawabin ne a gaban takwaransa na Burkina Faso’s, Kaftin Ibrahim Traoré da kuma na Mali, Kanal Assimi Goïta.

legitnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp