BBC ta kare shawarar da ta yanke cewa ba za ta kira ‘yan ta-da-ƙayar-baya na Hamas da sunan ”yan ta’adda’ ba, a cikin rahotannin da take yaɗawa game da hare-haren baya-bayan nan a Isra’ila.
Wani mai magana da yawun BBC ya ankarar da cewa akwai daɗaɗɗen matsayi da tashar labaran ta duniya ta ɗauka cewa masu aika rahotanninta, ba za su yi amfani da sunan ‘yan ta’adda ba, su a kan kansu, sai dai fa idan suna ruwaito zancen wani.
Wani daɗaɗɗen wakilin BBC kan harkokin waje, John Simpson ya ce “kiran wani da sunan ɗan ta’adda, na nuna cewa, kana goyon bayan wani ɓangare ne a cikin lamari”.
Sakataren tsaron Birtaniya Grant Shapps ya ce wannan manufa na “daf da zubar da mutuncin”, tashar kuma akwai buƙatar BBC ta gano inda ta ajiye “tunaninta na sanin ya kamata”.
Mai magana da yawun BBC na cewa: “BBC tashar labarai ce mai zaman kanta ta fuskar tsarin gabatar da aikin jarida, wadda aikinta shi ne ta bayyana haƙiƙanin abin da ke faruwa ‘a ƙasa’ ta yadda masu bibiyarmu za su iya yanke hukunci da kansu.”