fidelitybank

Ba za mu kirawo Falasɗinawa da sunan ƴan ta’adda ba – BBC

Date:

BBC ta kare shawarar da ta yanke cewa ba za ta kira ‘yan ta-da-ƙayar-baya na Hamas da sunan ”yan ta’adda’ ba, a cikin rahotannin da take yaɗawa game da hare-haren baya-bayan nan a Isra’ila.

Wani mai magana da yawun BBC ya ankarar da cewa akwai daɗaɗɗen matsayi da tashar labaran ta duniya ta ɗauka cewa masu aika rahotanninta, ba za su yi amfani da sunan ‘yan ta’adda ba, su a kan kansu, sai dai fa idan suna ruwaito zancen wani.

Wani daɗaɗɗen wakilin BBC kan harkokin waje, John Simpson ya ce “kiran wani da sunan ɗan ta’adda, na nuna cewa, kana goyon bayan wani ɓangare ne a cikin lamari”.

Sakataren tsaron Birtaniya Grant Shapps ya ce wannan manufa na “daf da zubar da mutuncin”, tashar kuma akwai buƙatar BBC ta gano inda ta ajiye “tunaninta na sanin ya kamata”.

Mai magana da yawun BBC na cewa: “BBC tashar labarai ce mai zaman kanta ta fuskar tsarin gabatar da aikin jarida, wadda aikinta shi ne ta bayyana haƙiƙanin abin da ke faruwa ‘a ƙasa’ ta yadda masu bibiyarmu za su iya yanke hukunci da kansu.”

latest news nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...
X whatsapp