fidelitybank

Ba za mu gajiya ba har sai mun murƙushe Lakurawa a Kebbi – Ƴansanda

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Kebbi, ta sha alwashin kawo karshen ‘yan fashi da miyagun laifuka a fadin jihar.

Hakan ya biyo bayan wani kazamin harin da wasu da ake zargin ‘yan kungiyar nan ne da ake kyautata zaton ‘yan kungiyar ta Lakurawa ne suka kai a karamar hukumar Augie, inda mutane 16 suka mutu.

A cikin wata sanarwa da rundunar ‘yan sandan jihar Kebbi ta fitar a ranar Litinin ta tabbatar da cewa ta tura tawagogin dabara domin farautar ‘yan ta’addan.

A cewar jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sanda, CSP Nafiu Abubakar, harin ya afku ne a ranar Asabar, 6 ga watan Afrilu, 2025, da misalin karfe 6 na yamma, yayin da wasu mahara dauke da muggan makamai suka afkawa wasu kauyuka biyu.

“Maharani wadanda suka isa wurin da yawan gaske, sun yi awon gaba da wasu shanu da ba a tantance adadinsu ba, suka kuma yi artabu da jama’ar yankin, wanda ya yi sanadin asarar rayuka goma sha shida,” in ji sanarwar.

Da yake Allah wadai da lamarin, kwamishinan ‘yan sanda, Bello Sani, ya bayar da tabbacin cewa za a yi adalci cikin gaggawa.

Ya sanar da tura karin tawaga masu dabara da suka hada da ‘yan sanda, sojoji, jami’an tsaron Najeriya da jami’an tsaro na farin kaya, da ‘yan banga zuwa yankunan da rikicin ya shafa.

“Kudirinmu na kawar da ‘yan fashi da sauran miyagun laifuka a Jihar Kebbi ya tsaya tsayin daka, muna tura duk wani abu da ake da shi don ganin an gurfanar da wadanda suka aikata wannan aika-aika a gaban kuliya,” in ji CP Sani.

CSP Abubakar ya kara da cewa tun daga lokacin an dawo da zaman lafiya a yankunan da lamarin ya shafa, kuma ana ci gaba da gudanar da cikakken bincike.

Rundunar ‘yan sandan ta kuma yi kira ga jama’a da su kwantar da hankalinsu, su kuma ci gaba da bayar da hadin kai ga jami’an tsaro, tare da jaddada aniyar ta na kare rayuka da dukiyoyi a fadin jihar Kebbi.

daily 
post news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp