Rundunar ‘yan sandan jihar Kebbi, ta sha alwashin kawo karshen ‘yan fashi da miyagun laifuka a fadin jihar.
Hakan ya biyo bayan wani kazamin harin da wasu da ake zargin ‘yan kungiyar nan ne da ake kyautata zaton ‘yan kungiyar ta Lakurawa ne suka kai a karamar hukumar Augie, inda mutane 16 suka mutu.
A cikin wata sanarwa da rundunar ‘yan sandan jihar Kebbi ta fitar a ranar Litinin ta tabbatar da cewa ta tura tawagogin dabara domin farautar ‘yan ta’addan.
A cewar jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sanda, CSP Nafiu Abubakar, harin ya afku ne a ranar Asabar, 6 ga watan Afrilu, 2025, da misalin karfe 6 na yamma, yayin da wasu mahara dauke da muggan makamai suka afkawa wasu kauyuka biyu.
“Maharani wadanda suka isa wurin da yawan gaske, sun yi awon gaba da wasu shanu da ba a tantance adadinsu ba, suka kuma yi artabu da jama’ar yankin, wanda ya yi sanadin asarar rayuka goma sha shida,” in ji sanarwar.
Da yake Allah wadai da lamarin, kwamishinan ‘yan sanda, Bello Sani, ya bayar da tabbacin cewa za a yi adalci cikin gaggawa.
Ya sanar da tura karin tawaga masu dabara da suka hada da ‘yan sanda, sojoji, jami’an tsaron Najeriya da jami’an tsaro na farin kaya, da ‘yan banga zuwa yankunan da rikicin ya shafa.
“Kudirinmu na kawar da ‘yan fashi da sauran miyagun laifuka a Jihar Kebbi ya tsaya tsayin daka, muna tura duk wani abu da ake da shi don ganin an gurfanar da wadanda suka aikata wannan aika-aika a gaban kuliya,” in ji CP Sani.
CSP Abubakar ya kara da cewa tun daga lokacin an dawo da zaman lafiya a yankunan da lamarin ya shafa, kuma ana ci gaba da gudanar da cikakken bincike.
Rundunar ‘yan sandan ta kuma yi kira ga jama’a da su kwantar da hankalinsu, su kuma ci gaba da bayar da hadin kai ga jami’an tsaro, tare da jaddada aniyar ta na kare rayuka da dukiyoyi a fadin jihar Kebbi.