fidelitybank

Ba za mu cigaba da yin rijista ba – INEC

Date:

Hukumar zaɓe ta kasa INEC, ta ce dokokin Kundin Tsarin Mulkin ƙasar ba su ba ta damar ta ci gaba da yin aikin rajistar kaɗa ƙuri’a ba kafin babban zaɓe na 2023.

A ranar Talata ne rahotanni suka ambato Babbar Kotun Tarayya a Abuja ta umarci hukumar ta ci gaba da aikin rajistar har zuwa saura kwana 90 kafin zaɓen.

Independent National Electoral Commission (INEC) ta rufe aikin rajistar zaɓen a watan Yuli da ya gabata, abin da ya jawo martani da koke-koke daga ƙungiyoyin farar hula cewa za a tauye wa miliyoyin ‘yan ƙasa haƙƙinsu.

Amma da yake magana ta cikin shirin Politics Today na kafar talabijin ta Channels TV a ranar Talata, Kwamashinan Wayar da Kan Masu Zaɓe na INEC Festus Okoye ya ce hukumar ba ta samu kwafin hukuncin ba tukunna.

Ya ƙara da cewa: “Abu ne da ba zai yiwu ba a tsarin Kundin Tsarin Mulki ga INEC ta ci gaba da aikin rajistar masu zaɓe.”

Ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoton, saura kwana 93 da awa 7 a fara kaɗa ƙuri’a a babban zaɓen da za a gudanar a watan Fabarairu, inda ‘yan Najeriya za su zaɓi shugaban ƙasa da gwamnoni da ‘yan majalisar tarayya da na jiha.

tribune

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Barrister Sa’idu ya kama aiki bayan ya maye gurbin Muhyi Magaji

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rantsar...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jami’ar Bayero ta Kano ta yi sabon shugaba

Farfesa Haruna Musa, ya karɓi ragamar shugabancin jami’ar Bayero...

Gwamnatin Kano ta amince Barau FC ta yi wasa a filin Sani Abacha

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kungiyar kwallon kafa...

Gwamnatin Tinubu na takalar Kwankwaso da fada – Buba Galadima

Jigo a jam'iyyar NNPP, kuma na hannun tsohon gwamnan...

Newcastle United ta dauki dan wasan tsakiya Jacob daga Aston Villa

Newcastle United ta sanar da daukar dan wasan tsakiya...

Hisba ta kama ‘yan Mata 62 da zargin aikata baɗala a Kano

Hukumar Hisbah ta kama mutane 62 kan zargin aikata...

NNPP ta yi tafka magudi a zabencike gurbin Kano – Farouk Lawan

Tsohon dan majalisar wakilai, Farouk Lawan, ya yi zargin...

Dan shugaban kungiyar Boko Haram ya shiga hannu

Hukumomi a ƙasar Chadi sun kama yaron shugaban ƙungiyar...
X whatsapp