fidelitybank

Ba za mu cigaba da tanka wa Wike ba – PDP

Date:

Jam’iyyar PDP, ta sha alwashin cewa, ba za ta ci gaba da yin tsokaci a kai-da-kai da gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike ke yi wa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Atiku Abubakar.

Ku tuna cewa Gwamna Wike wanda ya bukaci shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Iyorchia Ayu ya yi murabus a matsayin sharadin marawa Atiku baya a zaben da za a yi a watan Fabrairu, a lokuta da dama, ya tunkari tsohon mataimakin shugaban kasar.

A ranar Litinin, Wike, yayin da yake mayar da martani game da amincewa da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, Peter Obi da tsohon shugaban Atiku, Olusegun Obasanjo, ya yi, ya yi wa Atiku ba’a, yana mai cewa dole ne wani abu ya kasance ba daidai ba.

Da yake mayar da martani, PDP a wata sanarwa da kakakin kuma daraktan hulda da jama’a na kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na PDP, Sanata Dino Melaye, ya fitar dauke da sa hannun, ya bukaci Wike da ya ji kunya.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Ya kamata Wike ya ji kunya ganin yadda ya rika neman Atiku a kullum ta hanyar rashin mutuntawa da cin mutuncin mutumin da bai yi maka komai ba.

“Ina ba shi shawara da ya goyi bayan duk wanda yake so ya goyi bayan saboda ba za mu lamunta da son zuciya ba. Abin tambaya a nan shi ne, shin akwai wani abu da Wike bai damka wa Amaechi ba?

“Me yasa Prince Uche Secondus, Rt Hon. Austin Okpara, Sen. Lee Meaba, H:E Celestine Omehia, Chief Abiye Sikibo, Sen George Sekibo, Hon. Chinyere Igwe, da sauransu, sun bar shi da rashin sanin ya kamata ga Atiku. Tabbas wani abu ba daidai ba ne a wani wuri”.

legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp