fidelitybank

Ba za mu biya dan ta’adda kudin fansa ba – Tinubu

Date:

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya umarci jami’an tsaro da kada su biya kuɗin fansar sakin kusan ɗalibai 300 da malaminsu da aka yi garkuwa da su makon da ya gabata daga wata makaranta da ke Kaduna a yankin arewa maso yammacin ƙasar.

Tinubu ya kuma umarci hukumomin tsaro da su tabbatar an kuɓutar da dukkan mutanen da aka sace ba tare da biyan ƴan bindigar kuɗin fansa ba, kamar yadda ministan yaɗa labarai, Muhammed Idris ya shaida wa ƴanjarida a ranar Laraba.

Ministan ya ce shugaba Tinubu ya faɗa wa sojojin da ke laluben inda ɗaliban suke su tabbatar “ba a biya ko sisin kwabo ba”.

Tun farko, ƴan’uwan ɗaliban da ke tsaren sun ce ƴanbindiga sun buƙaci a biya su kuɗi mai yawa domin su saki yaran da suka sace daga makarantarsu a ƙauyen Kuriga.

Cikin makon da ya gabata, an sace mutane da dama ciki har da fiye da mutum 60 daga wani ƙauye a dai jihar ta Kaduna.

Cikin shekara uku da ta gabata, ɗaruruwan ɗalibai aka sace. Wasu a cikinsu an sake su bayan tattaunawa da hukumomi duk da cewa jami’ai sun musanta biyan kuɗin fansa.

Wata doka da aka amince da ita a 2022 ta hana biyan kuɗin fansa ga masu garkuwa.

Ƙaruwar sace-sacen mutane na zama ƙalubale ga gwamnatin Tinubu da ta yi alƙawarin magance matsalar tsaro.

legit ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp