Shugaban ƙungiyar Hezbollah, Hassan Nasrallah, ya ci alwashin hana Isra’ilawa komawa gidajensu a arewacin ƙasar.
Kusan mutum 60,000 ne suka gudu daga muhallansu daga arewacin Isra’ilar saboda hare-hare kusan kullum da ƙungiyar ke kaiwa yankin daga Lebanon maƙwabciyarta.
“Muna ganin su a matsayin ‘yan mamaya kuma masu kama wuri su zauna a gidajen Falasɗinawa,” a cewarsa cikin jawabin da ya kammala babu daɗewa.
“Kun ƙalubalance mu kuma mun amsa ƙalubalen. Ina faɗa wa Netanyahu da Gallant cewa ba za ku cim ma wannan muradin ba.
“Ba za ku iya mayar da mutanen nan arewaci ba. Hanya ɗaya da za ku iya yin hakan ita ce ku dakatar da hare-hare a kan Gaza da Gaɓar Yamma da Kogin Jordan. Ita ce hanyar kawai.”