fidelitybank

Ba za a shiga kangin yunwa a Najeriya ba – Minista

Date:

Ministan noma da raya karkara na kasa, Mohammed Abubakar, ya yi watsi da fargabar da ake yi a kasar na fuskantar karancin abinci cikin watanni masu zuwa.

Yayin da yake amsa tambayoyi daga ‘yan majalisa a wajen kare kasafin kudin hukumarsa a zauren majalisar dokokin kasar, ministan ya ce ba za su bari hakan ta faru ba.

Wasu daga cikin ‘yan majalisar dai sun bayyana cewa matsalar ambaliyar ruwa za ta shafi fannin noma a kasar.

Sun kara da cewa an yi hasashen cewar kasashen Afirka za su fuskanci karancin abinci sakamakon rashin shigo da abinci da yakin Ukraine ya haddasa.

To Amma ministan ya ce ”ba za mu bari matsalar karancin abinci ta yi tasiri a Najeriya ba, ina mai tabbatar muku da cewa da yardar Allah hakan ba za ta faru ba, saboda akwai matakai da dama da muka dauka domin magance wannan matsalar”.

Ya ci gaba da cewa ”daya daga cikin matakan da muka dauka shi ne noman rani, wanda muka ware masa kudi, muna aiki da ma’aikatar kudi, muna kuma samun tallafi daga cibiyoyin kudi, kamar bankin raya kasashen Afirka, dan haka za mu fadada noman ranin”.

Ministan ya kuma ce gwamnati na nazari kan irin barnar da ambaliyar ta haifar wa amfanin gona kamar shinkafa da masara, da kuma yawan manoman da lamarin ya shafa. kamar yadda kamfanin dillancin labaran kasar (NAN) ya ruwaito.

latest nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya ƙi amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na É—aukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

ÆŠanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa Æ´an Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa Æ´anbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen Æ™auyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faÉ—a ADC

Tsohon É—an jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...
X whatsapp