Babban hafsan hafsoshin soja, Janar Lucky Irabor, a ranar Lahadin da ta gabata ya tabbatar wa ‘yan kasa cewa, ba za a sake samun juyin mulki a Najeriya ba.
Irabor ya kuma ce rundunar sojin kasar za ta hada kai da ‘yan sanda wajen samar da tsaro a lokacin babban zabe.
Babban hafsan tsaron ya bayar da wannan tabbacin ne ga manema labarai a babban dakin taro na kasa da ke Abuja, a karshen taron tunawa da sojojin na shekarar 2023.
“Dimokradiyya ta zo ta tsaya; gwamnatin jama’a, ta jama’a da na jama’a ta zo ta zauna”, in ji shi.
Irabor ya bayyana cewa yana tattaunawa da Sufeto-Janar na ‘yan sanda don tsara hanyoyin da za a tabbatar da tsaro a zaben.
“Mun kuma yi abubuwan da ya kamata a bukaci mu ba da tallafi ga ‘yan sanda yayin da ake gudanar da zaben”, CDS ya kara da cewa.
A nasa jawabin, IGP Usman Baba ya jajantawa iyalan jami’an da suka mutu da na sojoji da ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro.
Baba ya shawarci ’yan Najeriya da su tabbatar da sadaukarwar da suke yi ba a banza ba ne yayin da “muna shiga ayyukan da za su ci gaba da inganta zaman lafiya da hadin kai, zaman lafiya”.