Tsohon Sanatan Kaduna ta tsakiya, Sanata Shehu Sani ya ce ba za a daina garkuwa da mutane a Arewa ba muddin Bello Turji da Ado Aleru na hannun su.
Sani dai na mayar da martani ne kan sace mutane 80 da aka yi a jihar Zamfara.
Ya jaddada cewa, gwamnati ta gaza wajen kare rayukan ‘yan Najeriya.
Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da yara sama da 80 a karamar hukumar Tsafe da ke jihar Zamfara.
Yaran da aka yi garkuwa da su ranar Juma’a ‘yan shekara 12 zuwa 17 ne.
Iyayen wadanda harin ya rutsa da su sun ce, da sanyin safiya ne maharan suka tare su suka tafi da su cikin dajin.
Da yake mayar da martani, Sani ya wallafa a shafinsa na Twitter cewa: “Yan ta’adda sun yi garkuwa da mutane 80 a jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya.
“Matukar dai irin su Bello Turji da Ado Aleru suna nan gaba daya duk da tashin bama-baman da jiragen ke yi, ba za a daina sace mutane a yankunan karkara ba. Gwamnati ta kasa tabbatar da rayuka. “