Ƙungiyar Hamas ta yi gargaɗin cewa babu wani da take garkuwa da shi da zai bar Gaza da ransa har sai an biya buƙatunmu.
Kakakin Hamas, Abu Obeida ne ya bayyana haka cikin wani saƙon murya da aka wallafa ranar Lahadi ta shafin Telegramt.
Ana i gaba da matsa wa Hamas lamba game da fiye da mutum 38 da har yanzu suke hannunta da wasu ƙungiyoyin masu riƙe da makamai.
Isra’ila ta sha yin alƙawarin yin duk bai yiwuwa na kuɓutar da sauran mutanen da ke hannun Hamas.
Mutum 110 aka saki a jumulla sai dai yarjejeniyar dakatar da yaƙi ta mako ɗaya wadda a ƙarƙashinta aka saki gommai ta zo ƙarshe kuma tun lokacin Isra’ila ta ci gaba da luguden wuta a Gaza.