fidelitybank

Ba wata sa’insa tsakanin Tinubu da Shettima – Fadar Shugaban Kasa

Date:

Fadar shugaban ƙasa ta ƙaryata zargin da ake na rashin jituwar da ke tsakanin shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da mataimakinsa Kashim Shettima, inda ta bayyana cewa dangantakar shugabannin biyu na nan da ƙarfinta.

Babban mataimaki na musamman kan harkokin yaɗa labarai da sadarwa ga mataimakin shugaban ƙasa, Stanley Nkwocha ne ya sanar da hakan a cikin wata sanarwar da ya fitar a bikin cika shekaru 58 na mataimakin shugaban ƙasar, Kashim Shettima.

Nkwocha ya bayyana zargin a matsayin “makirci mara tushe waɗanda ba su nuna gaskiyar lamari a Aso Rock”.

Sanarwar ta jaddada cewa Shettima wani muhimmin ɓangare ne na gwamnatin Tinubu inda yake bai wa Tinubu cikakken goyon baya da kuma ƙwarin gwiwa.

Talla

Da yake watsi da jita-jitar rashin jituwa tsakanin Tinubu da Shettima, Nkwocha ya sake nanata biyayyar Shettima ga gwamnatin Tinubu.

Ya bayyana kwazon Shettima da jajircewarsa ga shugaba Tinubu, inda ya bayyana cewa biyayyar mataimakin shugaban ƙasa da hadin gwiwarsu sun taimaka wajen samun kyakkyawan yanayi da hadin kai a cikin gwamnatin.

Da yake magana kan rahotannin cewa Shettima yana jinya, Nkwocha ya ce waɗannan ikirari ba su da tushe.

A ƙarshe ya jaddada irin gudummawar da Shettima ke bai wa gwamnatin Tinubu, inda ya nuna cewa mataimakin Shugaban kasa ya kawo wani nau’i na kwarewa da kuzari na musamman don tallafa wa manufofin Tinubu ga Najeriya.

legitnewsnigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp