fidelitybank

Ba wata mafaka da za ka samu Buhari – Sowore

Date:

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar African Action Congress, AAC, a zaben 2023, Omoyole Sowore, ya ce babu wata maboya da shugaban kasa Muhammadu Buhari zai samu bayan ya sauka.

Sowore ya ce dole ne Buhari ya girbi abun da ya shuka na cin zarafin dan Adam.

Ya na mai da martani ne kan kalaman Buhari na komawa Jamhuriyar Nijar bayan 29 ga Mayu.

Buhari ya sha alwashin komawa Jamhuriyar Nijar daga garin Daura na jihar Katsina idan har zaman lafiyarsa ya tabarbare.

Ya yi wannan jawabi ne a gidan gwamnatin jihar yayin da ya karbi bakuncin wasu mazauna babban birnin tarayya karkashin jagorancin minista Muhammad Musa Bello a wajen bikin sallar Eid-el-Fitr.

“Ba zan iya jira in koma gida Daura ba. Idan sun yi wata hayaniya ta dame ni a Daura, zan tafi Jamhuriyar Nijar. Da gangan na shirya don yin nisa sosai.

“Na sami abin da nake so kuma zan yi ritaya a nitse zuwa garinmu. Duk da fasahar zamani ba zai yi sauki ba zuwa Daura,” inji shi.

Da yake mayar da martani, Sowore ya ce komai dadewa za a sa Buhari ya biya kudin ta’asar da ya yi.

Sowore ya rubuta a shafinsa na Twitter cewa: “Shugaba @Mbuhari, ka yi hakuri, ba za a buya ga miyagu ba. Dole ne ku biya bashin da kuka aikata na cin zarafin bil’adama.

“Har Ĉ™arshen zamani, zaluntar ku za ta cinye ku. Komai tsawon lokacin da zai ɗauka, ba zai damu da inda kuka ɓoye ba, zaku amsa laifinku. #Revolution yanzu.”

nnn.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar Ĉ´ansandan jihar Kaduna, sun buĈ™aci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi Ĉ™ungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban Ĉ™aramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp