fidelitybank

Ba wata jam’iyyar da na ke goyon baya – Kwankwaso

Date:

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar New Nigeria Peoples Party, NNPP, Sen. Rabi’u Musa Kwankwaso ya karyata rade-radin da ake yadawa cewa yana yiwa wata jam’iyya aiki a zaben 2023 mai zuwa.

Kwankwasko ya bayyana haka ne a lokacin da yake amsa tambayoyi daga wasu magoya bayansa a lokacin da yake gabatar da shirin rediyo kai tsaye a birnin Dutse na jihar Jigawa.

Ya ce, tun lokacin da shi da magoya bayansa suka koma jam’iyyar NNPP, wasu mutane ke hada karairayi iri-iri saboda dalilansu na siyasa.

A cewarsa, “Na ji wasu na cewa dattawan Arewa sun gana da ni, sun ce in bar dan takarar Arewa, wasu kuma na cewa ina soyayya da APC.

“Wa zai iya gaya mana Arewa? Wa ya fi mu sanin Arewa? Waɗannan ‘yan takara ne waɗanda ke da matsala game da cancantar su da lafiyarsu. ”

Ya bayyana cewa wannan labarin ba shi da tushe balle makama kuma wasu bata gari ne suka shirya shi saboda wasu dalilai na siyasa domin su dauke hankalin ‘yan Najeriya.

“Allah ya kiyaye na yi aiki ko soyayya da APC, PDP, ina jam’iyyar NNPP ne, babu gudu babu ja da baya.

“Wannan wata dama ce ta zinari ga dukkan ‘yan Najeriya idan suna son abubuwa su canja da kyau. NNPP ita ce amsar kuma idan suna son abubuwa su ci gaba da kasancewa,” ya kara da cewa.

thisdaynews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Talauci da rashin tsaro na iya barazana ga zaɓen 2027 – Rahoto

Ƙungiyar fafutikar kare haƙƙin ɗan'adam da tabbatar da dimokuraɗiyya...

Tinubu ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan Dantata

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya aike da saƙon ta'aziyarsa...

Dangantaka tsakanin Amurka da Canada ta yi tsami

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai yanke dukkan...

An yi jana’izar Kwamandojin sojinta da masana nukiliyar Iran da Isra’ila ta kashe

Iran ta gudanar da jana'izar mutum 60, ciki har...

Za a binne Attaijirin dan kasuwar nan na Kano Dantata a Dubai

Allah ya yi wa attajirin ɗan kasuwar nan na...

Dalori ne ya maye gurbin Gnaduje a shugabancin APC

Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar...

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...
X whatsapp