Tsohon gwamnan jihar Kano kuma dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar New Nigeria Peoples Party, NNPP, Sen. Rabi’u Musa Kwankwaso ya karyata rade-radin da ake yadawa cewa yana yiwa wata jam’iyya aiki a zaben 2023 mai zuwa.
Kwankwasko ya bayyana haka ne a lokacin da yake amsa tambayoyi daga wasu magoya bayansa a lokacin da yake gabatar da shirin rediyo kai tsaye a birnin Dutse na jihar Jigawa.
Ya ce, tun lokacin da shi da magoya bayansa suka koma jam’iyyar NNPP, wasu mutane ke hada karairayi iri-iri saboda dalilansu na siyasa.
A cewarsa, “Na ji wasu na cewa dattawan Arewa sun gana da ni, sun ce in bar dan takarar Arewa, wasu kuma na cewa ina soyayya da APC.
“Wa zai iya gaya mana Arewa? Wa ya fi mu sanin Arewa? Waɗannan ‘yan takara ne waɗanda ke da matsala game da cancantar su da lafiyarsu. ”
Ya bayyana cewa wannan labarin ba shi da tushe balle makama kuma wasu bata gari ne suka shirya shi saboda wasu dalilai na siyasa domin su dauke hankalin ‘yan Najeriya.
“Allah ya kiyaye na yi aiki ko soyayya da APC, PDP, ina jam’iyyar NNPP ne, babu gudu babu ja da baya.
“Wannan wata dama ce ta zinari ga dukkan ‘yan Najeriya idan suna son abubuwa su canja da kyau. NNPP ita ce amsar kuma idan suna son abubuwa su ci gaba da kasancewa,” ya kara da cewa.