fidelitybank

Ba wani nadama da na yi sakamakon halin da Najeriya ta ke ciki – Buhari

Date:

Tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, ya bayyana damuwa game da wani labari da ake ta yayatawa, inda aka ruwaito, tsohon mai ba shi shawara na musamman kan harkokin watsa labarai, Mista Femi Adeshina wai yana cewa Buhari yana nadamar wasu abubuwan da ya yi a lokacin mulkinsa na shekara takwas.

Mai magana da yawun tsohon shugaban, Malam Garba Shehu, ya shaida wa BBC cewa, an yi wa bayanan na Mista Femi Adeshina gurguwar fahimta ko kuma an sa son zuciya wajen fassara abin da ya fada.

A dangane da hakan ne Garba Shehu ya ce ba a yi wa Femi Adesina adalci ba.

Kakakin ya ce, “ita wannan jarida da ta ɗauki kanun labaran ta buga so suke su jawo hankalin mutane su sai da jaridarsu in ba don haka ba me aka yi na aikin da-na-sani?”

Ya ce abin da tsohon shugaban ya yi a lokacin mulkin nasa na kalamai da ayyuka jama’a aka yi wa domin amfanin ƙasar ba son-rai ba saboda haka maganar da-na-sani ba ta ma taso ba a kan haka.

“Duk abin da zai yi iya ƙarfinsa da jinin jikinsa ya yi don ya kyautata ƙasar Najeriya don ya kyautata rayuwa ta al’ummar Najeriya,” ya ce.

Ya ce akwai ayyuka da dama a fanni daban-daban da shugaban ya yi ana gani.

Ya koka da cewa, “Amma dama ƙasar haka ta gada idan giwa ta faɗi aka ce ai kowa ma wuƙarsa zai zaro ya ce bari ya zo ya yanka.”

“Amma Shugaba Muhammadu Buhari ya yi rawar-gani kuma idan ba a faɗa yau ba nan gaba wataƙila wasu za su zo bayanmu su duba su yi mana adalci su ce ga abin da ya yi na alheri a ƙasar nan,” in ji kakakin.

Martani kan zargin jefa ƙasa cikin matsaloli

Dangane ya yadda ake zargin cewa gwamnatin Buharin ita ce sanadin halin da ƙasar take ciki a yanzu na wasu katutun matsaloli sai kakakin ya ce, ai daman a duk duniya babu wata gwamnati daya da za ta iya magance matsalolin ƙasa gaba ɗaya sai dai ta yi iya ƙokarinta ta tafi wata ta zo ta ɗora a ciyar da ƙasar gaba.

Ya ce, “Idan har an samu takura ko wani matsatsi dubawa za a yi a ga shin mene ne ya kawo wannan matsala.”

“Ba a taɓa samun wata gwamnati a ƙasar nan da ta samu kanta a karayar tattalin arziƙi irin lokacin Shugaba Muhammadu Buhari ba sabili da dogaro da muke yi da man fetur ya karye a duniya cutar Korona ta zo kowa ce ƙasa ta garƙame ƙofarta ta rufe tattalin arziƙi ya sake nutsewa,” in j shi

“Amma Alhamdulillahi sai da ya cicciɓo tattalin arziƙin Najeriya aka fitar da shi daga cikin wannan mawuyacin hali,” a cewar kakakin.

Garba Shehu ya ce suna alfahari da cewa babu wani sashe na Najeriya da ba za a ga wasu ayyuka na cigaban ƙasa da gwamnatin Buhari ta yi ba.

Ya ce, “muhimman ayyuka na raya ƙasa da tsohon Shugaba Muhammadu Buhari ya yi don kyautata wa al’umma ai kamar ruwan sama ne in ma bai buge ka a gona ba zai buge ka a gida.”

legit nig. news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...
X whatsapp