fidelitybank

Ba wani muƙami da na ke nema a wajen Tinubu – El-Rufa’i

Date:

Gwamnan Jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai, ya musanta jita-jitar da wasu ke yi cewa, yana sha’awar kujerar shugaban ma’aikata a sabuwar gwamnatin zababben shugaban Bola Ahmed Tinubu da za a kafa karshen watan Mayun shekarar na ta 2023.

Gwamna El-Rufai ya musanta rade-raden ne ranar Asabar a jihar Gombe yayin tattaunawa da manema labarai.

Gwamnan ya je jihar ta Gombe ne domin kaddamar da aikin gina gidaje 550 da gwamnan jihar Muhammad Inuwa Yahaya zai yi.

El-Rufai ya ce hasashen da mutane ke yi maganganu ne kawai na kan titi.

Ya kara da cewa ba dole ne sai mutum ya kasance cikin gwamnati ba kafin ya taimaka wajen ci gaban Najeriya, don haka ko baya cikin gwamnati zai dukufa wajen ciyar da ita gaba a cewarsa.

“Ban tattauna da zababben shugaban kasa kan wannan batun ba don haka ba na son jita-jita.

“Na karanta yadda ake ta danganta ni da mukamai daban-daban a wasu jaridu, to amma kun san ni dan Najeriya ne da ya dukufa wajen ciyar da ita gaba” in ji El-Rufai.

legit latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp