Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya haramta tafiye-tafiye zuwa ƙasashen waje na tsawon wata uku ga ministoci da shugabannin ma’aikatu da hukumomin gwamnati.
Shugaban ma’aikata a fadar shugaban ƙasa, Femi Gbajabiamila ne ya sanar da umarnin cikin wata takarda da aka aikewa sakataren gwamnatin tarayya, George Akume.
An bayyana ƙalubalen tattalin arzikin da ake fama da shi da buƙatar alkinta kuɗin gwamnati da ake kashewa yayin irin waɗan nan tafiye-tafiye a matsayin dalilan da suka sa aka ƙaƙaba haramcin kan tafiye-tafiye zuwa ƙasashen waje.
Takardar ta ce jami’i na buƙatar amincewar shugaban ƙasa idan yana son a ɗage masa haramcin kuma dole a yi hakan mako biyu kafin lokacin tafiyar.
Matakin na zuwa ne bayan bulaguron baya-bayan nan da ofishin akanta janar na ƙasa ya yi da ta janyo cece-kuce.
Ofishin ya gudanar da wani taron ƙarawa juna sani a birnin Landan wanda ya samu halartar kwamishinonin kuɗi da jami’ai daga ofishin akanta janar.
A baya dai al’umma sun yi ta tsokaci a kai, abin da suka ce ya zo ne a lokacin da ƙasar ke fuskantar ƙalubalen tattalin arziki da kuma tashin dala da ke shafar darajar kuɗin naira.