fidelitybank

Ba wanda zai ƙara shigowa Kano ya yi fim ko TikTok a Kano – Majalisa

Date:

Majalisar dokokin jihar Kano ta amince da yi wa dokar da ta kafa hukumar tace fina-finai gyaran fuska.

Cikin gyare-gyaren har da tilasta wa masu wuraren da ake gudanar da bukukuwa da taruka wato event centres yin rajista.

Ayyukan hukumar na ɗaukar hankali musamman a arewacin Najeriya saboda yadda ake kai ruwa rana tsakaninta da masu shirya finafinai.

Majalisar ta amince da gyaran dokar ne wadda aka kafa tun 2001 saboda yadda ɗaukar finafinai ya sauya, abin da ya sa majalisar ta ce tilas sai ana taka wa lamarin birki a wasu abubuwan don kare addini da kuma al’adu.

“Yanzu hukumar ta kara samun iko a kan abubuwa da dama,” a cewar shugaban masu rinjaye na majalisar Lawal Husaini Dala.

Ya ce daga yanzu babu wanda zai shigo birnin Kano ya yi ta ɗaukar fim ba tare da samun izinin hukumar ba.

A nasa ɓangare, shugaban hukumar tace fina-finan ta jihar Kano Abba El-Mustapha, ya ja hankalin masu wallafa bidiyo a kafofin sada zumunta waɗanda ake kira da content creators da su guji duk abin da zai taɓa mutuncin addini ko na al’adar bahaushe ko kuma al’ummar jihar Kano.

Ya ce za su mara wa waɗanda ke bidiyo don nishaɗi ko samun arziki, amma ba zagin mutane ba.

Bugu da ƙari, El-Mustapha ya ce ƴan social media su sani cewa hukumar tace fina-finai tana da hurumi kan dukkan wani abu da ya saɓa wa addini da al’adu, inda ya ce muddin suka samu korafi akan wani bidiyo ko wani abu da aka saka a shafukan sada zumunta, to za su ɗauki mataki.

Bayanai na cewa kawo yanzu dai majalisar dokokin jihar ta Kano ta kammala na ta aikin na amincewa da gyaran dokar hukumar, abin da ya rage yanzu shi ne gwamnan Kano ya sanya hannu a kai, amma babu tabbas ko zuwa yaushe ne zai yi hakan.

legit new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...
X whatsapp