fidelitybank

Ba wanda zai ƙara shigowa Kano ya yi fim ko TikTok a Kano – Majalisa

Date:

Majalisar dokokin jihar Kano ta amince da yi wa dokar da ta kafa hukumar tace fina-finai gyaran fuska.

Cikin gyare-gyaren har da tilasta wa masu wuraren da ake gudanar da bukukuwa da taruka wato event centres yin rajista.

Ayyukan hukumar na ɗaukar hankali musamman a arewacin Najeriya saboda yadda ake kai ruwa rana tsakaninta da masu shirya finafinai.

Majalisar ta amince da gyaran dokar ne wadda aka kafa tun 2001 saboda yadda ɗaukar finafinai ya sauya, abin da ya sa majalisar ta ce tilas sai ana taka wa lamarin birki a wasu abubuwan don kare addini da kuma al’adu.

“Yanzu hukumar ta kara samun iko a kan abubuwa da dama,” a cewar shugaban masu rinjaye na majalisar Lawal Husaini Dala.

Ya ce daga yanzu babu wanda zai shigo birnin Kano ya yi ta ɗaukar fim ba tare da samun izinin hukumar ba.

A nasa ɓangare, shugaban hukumar tace fina-finan ta jihar Kano Abba El-Mustapha, ya ja hankalin masu wallafa bidiyo a kafofin sada zumunta waɗanda ake kira da content creators da su guji duk abin da zai taɓa mutuncin addini ko na al’adar bahaushe ko kuma al’ummar jihar Kano.

Ya ce za su mara wa waɗanda ke bidiyo don nishaɗi ko samun arziki, amma ba zagin mutane ba.

Bugu da ƙari, El-Mustapha ya ce ƴan social media su sani cewa hukumar tace fina-finai tana da hurumi kan dukkan wani abu da ya saɓa wa addini da al’adu, inda ya ce muddin suka samu korafi akan wani bidiyo ko wani abu da aka saka a shafukan sada zumunta, to za su ɗauki mataki.

Bayanai na cewa kawo yanzu dai majalisar dokokin jihar ta Kano ta kammala na ta aikin na amincewa da gyaran dokar hukumar, abin da ya rage yanzu shi ne gwamnan Kano ya sanya hannu a kai, amma babu tabbas ko zuwa yaushe ne zai yi hakan.

today daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...
X whatsapp