fidelitybank

Ba wanda za mu kara sakin Isra’ilawa ba har sai an daina yaki – Hamas

Date:

Hamas ta ce ba za ta ƙara sakin ƴan Isra’ila da take garkuwa da su ba har sai an tsayar da yaƙi.

Hamas ɗin ta ce ƙungiyoyin Falasɗinawa sun dakatar da shirin sakin ƙarin mutane har sai Isra’ila ta amince ta kawo karshen yaƙi a Gaza.

A wani sako cikin harshen Larabci da Hamas ta fitar a shafin Telegram, ta ce: “Akwai matakin da Falasɗinawa suka ɗauka na ƙasa baki-ɗaya cewar babu wata tattaunawa kan musayar fursunoni da waɗanda ake garkuwa da su har sai bayan Isra’ila ta amince ta kawo karshen yaƙi.”

Ba a dai san wasu ɓangarori ne na Falasɗinawa be ke da alaka da wannan sanarwa.

Islamic Jihad, wata karamar ƙungiya a Zirin Gaza, ita ma tana rike da wasu ƴan Isra’ila.

Ana ci gaba da tattaunawa don cimma sabon yarjejeniya kan yaƙin a Alkahira, babban birnin Masar, duk da cewa tattaunawa da aka yi da farko ba ta cimma komai ba, inda aka ruwaito Hamas na cewa ba za su amince da wata yarjejeniyar tsagaita wuta na wucin-gadi ba.

Lokacin da aka tsagaita wuta na kwanaki shida a watan Nuwamba, an saki ƴan Isra’ila 105 da ake garkuwa da su bayan musaya da Falasɗinawa da ake tsare da su a gidajen yarin Isra’ila.

An yi imanin cewa har yanzu akwai ƴan Isra’ila 120 da ake rike da su a Gaza.

Isra’ila ta sha kin amincewa da yarjejeniyar tsagaita na dindindin da Hamas, inda ministan tsaron Isra’ila Itamar Ben Gvir, ya ce tsagaita wuta kafin karya lagon Hamas da kuma mayar da dukkan waɗanda ake garkuwa da su da cewa zai zama gazawa.

the nation newspaper nigeria today latest

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp