fidelitybank

Ba shugaban da zai iya kawo karshen ta’addanci a Najeriya – Lai

Date:

Ministan yada labarai da raya al’adu, Lai Mohammed, ya ce babu wani shugaba da zai ce shi ne zai iya kawo karshen ayyukan ’yan ta’adda a shekara mai zuwa.

Ministan ya yi wannan kakkausar martanin ne bayan an tambaye shi a wani taron manema labarai, cewa ko kalubalen tsaron da a ke fuskanta a halin yanzu zai kawo karshe kafin shugaba Buhari ya sauka daga mukamin sa a shekarar 2023. A cewar Aminiya.

Lai Mohammed sai ya ce,”Ba na tsammani ko shugaba Buhari ba shi da tabbacin cewar za a iya murkushe ayyukan ’yan bindiga a shekara mai zuwa, kuma zargin da a ke yi wa shugaba Buhari na rashin katabus wajen kare rayukan al’umma da a ke kashewa kusan a kullum”.

A makon nan ne dai, tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya bayyana cewa, Buhari ya yi iya kokarinsa, babu wani abin da zai iya tabukawa fiye da hakan a nan gaba.

Matsalar tsaro dai a Najeriya ta yi kamari sosai, musamman a yankin Arewacin Najeriya, inda ta sa mutane da dama fusata har a ka shiga yi wa Buhari zanga-zanga, domin kawo karshen zubar da jinin al’umma da a ke yi a yankin.

latest legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp