Ministan yada labarai da raya al’adu, Lai Mohammed, ya ce babu wani shugaba da zai ce shi ne zai iya kawo karshen ayyukan ’yan ta’adda a shekara mai zuwa.
Ministan ya yi wannan kakkausar martanin ne bayan an tambaye shi a wani taron manema labarai, cewa ko kalubalen tsaron da a ke fuskanta a halin yanzu zai kawo karshe kafin shugaba Buhari ya sauka daga mukamin sa a shekarar 2023. A cewar Aminiya.
Lai Mohammed sai ya ce,”Ba na tsammani ko shugaba Buhari ba shi da tabbacin cewar za a iya murkushe ayyukan ’yan bindiga a shekara mai zuwa, kuma zargin da a ke yi wa shugaba Buhari na rashin katabus wajen kare rayukan al’umma da a ke kashewa kusan a kullum”.
A makon nan ne dai, tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya bayyana cewa, Buhari ya yi iya kokarinsa, babu wani abin da zai iya tabukawa fiye da hakan a nan gaba.
Matsalar tsaro dai a Najeriya ta yi kamari sosai, musamman a yankin Arewacin Najeriya, inda ta sa mutane da dama fusata har a ka shiga yi wa Buhari zanga-zanga, domin kawo karshen zubar da jinin al’umma da a ke yi a yankin.