Asiwaju Bola Tinubu, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC), ya yi watsi da duk wata cece-ku-ce da ake ta yadawa a alakar sa da shugaban kasa Muhammadu Buhari, inda ya jaddada goyon bayansa ga shugaban kasa.
Tinubu ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi a taron jam’iyyar APC a Gusau, babban birnin jihar Zamfara, ranar Asabar.
Tsohon gwamnan na jihar Legas ya kuma yi alkawarin magance matsalolin da suka addabi jihar da kuma bunkasa noma.
Tinubu ya godewa al’ummar jihar Zamfara da manyan jiga-jigan jam’iyyar bisa kyakkyawar tarbar da suka yi da kuma ci gaba da goyon bayansu ga jam’iyyar APC.
Ya ce, “Na goyi bayan Shugaba Buhari tun kafin ranar farko da ya hau mulki. Zan ci gaba da zama mai goyon bayansa kuma abokinsa bayan kwana na karshe a ofis.
“Ya magance matsalolin da sauran shugabannin suka gudu daga gare su. Ya sami wani matsayi a tarihi wanda ba za a iya hana shi ba.
“Na fadi haka a baya, kuma yanzu zan sake cewa: idan aka rubuta ainihin tarihin wannan lokaci, shugaba Buhari za a yi masa alheri sosai saboda irin gudunmawar da ya bayar ga kasa.”
Tinubu ya kuma ce Buhari da Gwamna Bello Matawalle sun yi iyakacin kokarinsu wajen ganin an kawo karshen matsalar ‘yan fashi, inda ya yi alkawarin karfafa nasarorin da aka samu.
Ya kara da cewa, “Tsarin tsaro na zai baiwa dukkan sassan jami’an tsaro karfin gwiwa. Za mu yi amfani da fasahar zamani ta iska da ta kasa don ganowa da kama wadannan masu laifi.”