Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmad Lawan, ya karyata rahoton da ke yawo cewa, ya yi watsi da matakin da ya dauka a baya na kin daukaka kara kan hukuncin da babbar kotun tarayya da ke Damaturu ta yanke wanda ya soke zabensa.
Lawan a cikin wata sanarwa ta hannun mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Ola Awoniyi ya bayyana rahoton a matsayin ‘karya ce.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Wannan wani sabon labari ne daga masu yada labaran karya Sahara Reporters.”
Sanarwar ta kuma bayyana cewa, idan wani bai gamsu ba kuma ya yanke shawarar kalubalantar hukuncin da kotun ta yanke, to babu ruwansa da shugaban majalisar dattawa.
“A karo na goma sha uku, muna so mu jaddada cewa shugaban majalisar dattawa ba shi da niyyar daukaka kara a kan hukuncin kotun”, in ji sanarwar.
A cewar sanarwar shugaban majalisar dattawan ya bayyana nasa matsayin a fili kuma tuni ya ci gaba. “Shi mutum ne mai maganarsa”.
Don haka, ta bukaci jama’a da su ba da rahoton na bogi ba komai ba illa raini da ya kamace shi.
Ku tuna cewa jam’iyyar APC reshen jihar Yobe ta sha alwashin daukaka kara kan hukuncin da babbar kotun tarayya ta yanke, wanda ta bayyana Bashir Machina a matsayin dan takarar Sanatan Yobe ta Arewa.