fidelitybank

Ba ni da niyyar daukaka kara a kan hukuncin kotu – Ahmed Lawan

Date:

Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmad Lawan, ya karyata rahoton da ke yawo cewa, ya yi watsi da matakin da ya dauka a baya na kin daukaka kara kan hukuncin da babbar kotun tarayya da ke Damaturu ta yanke wanda ya soke zabensa.

Lawan a cikin wata sanarwa ta hannun mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Ola Awoniyi ya bayyana rahoton a matsayin ‘karya ce.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Wannan wani sabon labari ne daga masu yada labaran karya Sahara Reporters.”

Sanarwar ta kuma bayyana cewa, idan wani bai gamsu ba kuma ya yanke shawarar kalubalantar hukuncin da kotun ta yanke, to babu ruwansa da shugaban majalisar dattawa.

“A karo na goma sha uku, muna so mu jaddada cewa shugaban majalisar dattawa ba shi da niyyar daukaka kara a kan hukuncin kotun”, in ji sanarwar.

A cewar sanarwar shugaban majalisar dattawan ya bayyana nasa matsayin a fili kuma tuni ya ci gaba. “Shi mutum ne mai maganarsa”.

Don haka, ta bukaci jama’a da su ba da rahoton na bogi ba komai ba illa raini da ya kamace shi.

Ku tuna cewa jam’iyyar APC reshen jihar Yobe ta sha alwashin daukaka kara kan hukuncin da babbar kotun tarayya ta yanke, wanda ta bayyana Bashir Machina a matsayin dan takarar Sanatan Yobe ta Arewa.

nigeria newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin Æ´an Æ™asarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a Æ™yale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maÆ™ale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi É—an shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin Æ´an Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taÉ“a barin Iran ta Æ™era makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp