Gwamnan jihar Bauchi Sanata Bala Abdulkadir Mohammed, wato daya daga cikin masu neman takarar shugaban kasa a jam`iyyar PDP a Najeriya, ya ce da so samu ne zai so a ce sun cimma maslaha a tsakanin junansu wato `yan takara daga arewa, amma idan ta gagara baya fargabar shiga a yi zaben fidda gwani a tsakaninsu.
Gwamnan yana mai da martani ne ga matakin da takwaransa gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal, wanda ya ce maganar sulhu ta cije, kuma bai yarda da wata kuri`ar da wasu dattawa suka kada karkashin jagorancin Janar Ibrahim Babangida mai ritaya ba, inda suka zabi Sanata Bala Mohammed da tsohon shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki.
Gwamnan ya ce,” Idan an ce sulhu ya kakare, to ko me kakarewar dai an fito da sakamako, to amma duk da haka tun da ya kakare to ba wanda ya ke tsoron shiga takara, ni ban taba jin tsoron mutane ko kuma dan takara ba.”
Sanata Bala Mohammed ya ce duk wanda zai fito ya yi takara sai ya ci gaba, to amma sun gode wa dattawan arewa da suka yi musu sulhu, kuma sun ce duk wanda bai yarda ba yana iya zuwa ya ci gaba da neman takararsa.