fidelitybank

Ba na tsoron daukaka karar NNPP – Gawuna

Date:

Dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a zaben gwamnan jihar Kano da a ka yi a ranar 18 ga watan Maris, Nasir Yusuf Gawuna, ya ce ba ya jin tsoron daukaka karar da ke kalubalantar nasarar da ya samu a kotun ba.

A ranar Laraba ne kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan Kano ta bayyana jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben tare da korar Gwamna Abba Kabir Yusuf.

Kwamitin mai mutum uku ya bayar da umarnin a ba wa Gawuna takardar shedar dawowar sa da kuma janye takardar shaidar dawowa da aka baiwa Yusuf.

Kotun ta yi nuni da cewa, ba a buga tambari ko sanya hannu a katin zabe na kuri’u 165,663 ba, don haka, ba su da inganci kuma ta cire kuri’u 165,663 daga jimillar Yusuf.

Gawuna da ya ke zantawa da BBC Hausa a wata hira da ya yi da shi yayin da yake tsokaci kan hukuncin da kotun ta yanke, Gawuna ya ce, “Ina godiya ga Allah da ya ba mu nasara a zaben Jihar Kano, wanda kotu ta tabbatar a yau (Laraba). Ina gode masa domin nufinsa, wanda ya zabe mu mu yi jagoranci. Ina kuma gode wa lauyoyinmu da sauran jama’a bisa addu’o’i da goyon bayansu.”

Ya kara da cewa tun da farko an ayyana jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) a matsayin wadda ta lashe zaben amma ya yi imanin cewa Allah ya riga ya yanke hukunci, yana mai cewa suna da hakkin kalubalantar sakamakon a kotu, kuma sun yi hakan.

Gawuna ya ce duk wanda ya yarda cewa babu abin da ke faruwa ba tare da yardar Allah ba, ba zai taba damuwa ko daukar mulki a matsayin abin yi ko a mutu ba, yana mai jaddada cewa duk abin da ya same su, sun yi imani da nufin Allah ne.

A cewarsa, “Ba ma tsoro ko tsoro, domin mun san cewa duk abin da ya faru yana da kyau. Allah ba ya yin kuskure.”

latest legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar Ĉ´ansandan jihar Kaduna, sun buĈ™aci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi Ĉ™ungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban Ĉ™aramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp