Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce ba ya sha’awar tsayawa takarar shugaban ƙasa domin fafatawa da Shugaba Bola Tinubu a zaɓen 2027 mai zuwa.
Yahaya Bello ya bayyana haka ne a wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Michael Ohiare ya fitar, inda a ciki ya ce Yahaya Bello ya yi mamakin ganin wani faifan bidiyon da ake yaɗawa na yaƙin zaɓensa na 2022, amma ake cewa ya fara kamfe ne na zaɓen 2027 kamar yadda jaridun Najeriya suka ambato.
Sanarwar ta ce, “yayin da muke bayyanawa ƙarara cewa Yahaya Bello ba shi da burin takarar shugaban ƙasa a 2027, muna ƙara jaddada matsayarmu na goyon bayan sake zaɓar Tinubu a 2027”, in ji shi.
Mista Ohiare ya bayyana masu yaɗa labarin da ”masu yaɗa ƙarya”, waɗanda ba su da aikin yi sai ƙirƙirar ƙarya da yaɗa ta.
Yahaya Bello dai ya yi takarar shugabancin ƙasa 2023, kodayake ya daga baya ya janye a lokacin zaɓen fitar da gwani.