Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Babachir Lawal, ya musanta ikirarin cewa, yana cikin kwamitin da ya ba da shawarar a tsayar da wadanda za su tsaya takara ga Bola Tinubu.
A zantawarsa da Aminiya a daren Laraba, Lawal ya ce, ba ya cikin duk wani kwamitin da ya ba da shawarar a mika sunayen wadanda za su tsaya wa Tinubu.
Ya tabbatar da cewa, shi ne ya jagoranci kwamitin tsare-tsare da dabaru da aka kafa domin aiwatar da dabarun da Tinubu zai dauka na karbar tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC.
Ya kuma ce, bai san da wani karamin kwamiti da ya ba tsohon gwamnan Legas shawarar abokan takararsa ba.