Gwamnan jihar Ribas Nyesom Wike, ya ce baya da niyyar zama minista bayan ya rike mukamin gwamna.
Hakan dai na zuwa ne duk da rahotannin da ke cewa mukamin minista na daya daga cikin bukatun da sansaninsa ke nema a matsayin wani bangare na sharuddan yin aiki da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar.
Wike ya bayyana haka ne a lokacin kaddamar da sabon dakin shakatawa na VIP da aka gina a filin jirgin sama na Port Harcourt Omagwa ranar Talata.
Ya ce “Mutum daya ne kadai zai iya zama minista daga jiha, ba zan zama minista ba. Na ki. Ni ba abin zargi ba ne, Jihar Ribas dukiya ce.
“Don haka idan ba ku son cin zabe, aikinku ne. Ba ni ne ke gudanar da zaben ba.
“Wanda ya sanya takalmi ya san inda yake tsunkule shi”.
Don haka a bar Jihar Ribas ta ci gaba da yin abin da suke yi ta hanyar amfani da ayyukanmu wajen yi wa jama’armu kamfen.
Gwamnan ya kuma kalubalanci shugabannin jam’iyyar PDP na jihar da su dawo gida su yi wa dan takararsu na shugaban kasa yakin neman zabe, maimakon su rika yada jita-jita a Abuja.
“Kuna son goyon bayan dan takara, ba a gida kuke Abuja.
“Ku zo gida ku yi yakin neman zabe a yi wa jam’iyya aiki.