Gwamnonin jihohin Najeriya 36 sun ce, sun yi mamakin yadda ƙaramin Ministan Kasafin Kuɗi da Tsare-Tsare na ƙasa, Clem Agba ya zarge su da jefa Najeriya cikin talauci.
A watan Nuwamba ne Hukumar ƙididdiga ta Najeriya ta ce mutum miliyan 130 ne a ƙasar ke fama da talauci, kusan kashi 63 cikin 100 na a’umar ƙasar.
To sai dai a wata sanarwa da ƙungiyar gwamnonin ƙasar suka fitar mai ɗauke da sa hannun daraktan yaɗa labaran ƙungiyar Abdulrazaque Bello-Barkindo, ta bayyana kalaman ministan da cewa abu ne da bai kamata ba, kuma babu kanshin gaskiya a cikin kalaman ministan.
Gwamnonin sun ce iƙirarin da ministan ya yi cewa gwamnonin sun yi watsi da al’ummar karkara – ba shi da tushe balle makama.
A cikin makon da ya gabata ne dai ƙaramin ministan Kasafin Kuɗi da Tsare-Tsare Clem Agba a wani taro da ya yi da manema labarai bayan taron majalisar zartarwa ya ɗora alhakin katutun talaucin da ke damun ƙasar kan gwamnonin jihohi