Sanata Abdullahi Adamu, shugaban jam’iyyar APC na kasa, ya amince cewa zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya da aka yi a ranar 25 ga watan Fabrairu bai yi musu yadda suke so ba.
Adamu ya yi wannan jawabi ne a yammacin ranar Litinin a lokacin da yake gabatar da jawabinsa a taron kwamitin ayyuka na jam’iyyar APC na kasa tare da Bola Tinubu, zababben shugaban kasa, Kashim Shettima, mataimakin shugaban kasa, da kuma zababbun ‘yan majalisar wakilai ta kasa.
Taron na sirri wanda aka fara da misalin karfe 2:50 na rana, an gudanar da shi ne a dakin taro na Banquet House dake Abuja.
Karanta Wannan: Dogara ya magantu a kan batun komawarsa APC
Da yake jawabi a wajen taron, Adamu ya kuma taya daukacin zababbun jiga-jigan siyasa murna, inda ya jaddada cewa sun cancanci farin ciki da nasara bayan lashe zaben da aka yi a ranar 25 ga watan Fabrairu.
Adamu ya ce, “Ina matukar taya daukacin manyan mutane maza da mata da aka zaba. Ina gaisheku baki daya. Ku ne sabuwar tawagar Najeriya. Daga ranar 29 ga watan Mayu na wannan shekara, nauyin hadin kan kasarmu, zaman lafiya, da ci gabanmu zai rataya a wuyanku a matsayin kungiya.
“Yana da kyau da daraja a yarda cewa zaben na ranar 25 ga watan Fabrairu bai cika ba. Ba mu shirya gudanar da cikakken zabe ba.
“Tarihi na duniya ba shi da wani yanayi na cikakken zaɓe. Kamar sauran al’ummomin dimokuradiyya, mun himmatu wajen gudanar da zabubbuka masu inganci da gaskiya. Wannan mun yi.
“Daga sakamakon zaben ranar 25 ga watan Fabrairun 2023, babban zaben da hukumar zabe ta INEC ta sanar zuwa yanzu, jam’iyyar APC ta lashe zaben shugaban kasa, tsafta da kuma rinjaye a majalisun tarayya biyu.”