fidelitybank

Ba mu yarda Tinubu ya afkawa Nijar ba – Sanatocin Arewa

Date:

Kungiyar Sanatocin Arewacin Najeriya ta ce ba ta goyon bayan amfani da karfin soji don tilasta wa sojojin Nijar mayar da mulki ga hamɓararren shugaban ƙasar Mohamed Bazoum.

Mai magana da yawun ƙungiyar, Sanata Abdurrahman Kawu sumaila ya shaida wa BBC cewa, duk da cewa sanatocin ba su goyi bayan juyin mulkin da sojojin na Nijar suka yi ba, to amma kuma ba su goyi bayan amfani da karfin soji da ƙungiyar Ecowas ke shirin ɗauka kan Nijar din ba.

”Muna so ne a yi amfani da hanyoyin diplomasiyya wajen warware wannan matsala, amma ba ƙarfin soji ba”, in Sanata Kawu Sumaila.

Ya ƙara da cewa ƙungiyarsu tana la’akari da kusancin Nijar da Arewacin Najeriya

“‘jihohin Najeriya kusan guda bakwai duk sun yi iyaka da Nijar kuma kusan duka waɗannan jihohi, akwai matsalolin tsaro, kama daga na Boko-Haram zuwa na ‘yan fashin daji”.

”Idan muka bari aka fara yaƙi tsakanin Najeriya da Nijar to masifar da Najeriya za ta shiga, ita kanta Nijar dinma ba za ta shiga wanna masifa ba”, in ji Sanatan da ke wakilar Kano ta Kudu.

Sanata Kawu Sumaila ya ce hakan zai sa ‘yan ta’addan take waɗannan yankuna su ƙara samun dama wajen ci gaba da ɓarnar da suke gudanarwa.

Ya ƙara da cewa ”kuma yanzu halin da talakawan ƙasar nan ke ciki na matsin rayuwa da sauran matsaloli, idan aka fara yaƙin gaskiya yankunan Najeriya da ke iyaka da Nijar za su sake shiga cikin wata masifa”.

A ranar Juma’a ne shugaban Najeriya Bola Tinubu, kuma shugaban Ecowas, ya aike wa Majalisar Dattawan Najeriya buƙatar amincewarta domin tura sojojin ƙasar zuwa Jamhuriyar Nijar.

the punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...
X whatsapp