Kungiyar Sanatocin Arewacin Najeriya ta ce ba ta goyon bayan amfani da karfin soji don tilasta wa sojojin Nijar mayar da mulki ga hamɓararren shugaban ƙasar Mohamed Bazoum.
Mai magana da yawun ƙungiyar, Sanata Abdurrahman Kawu sumaila ya shaida wa BBC cewa, duk da cewa sanatocin ba su goyi bayan juyin mulkin da sojojin na Nijar suka yi ba, to amma kuma ba su goyi bayan amfani da karfin soji da ƙungiyar Ecowas ke shirin ɗauka kan Nijar din ba.
”Muna so ne a yi amfani da hanyoyin diplomasiyya wajen warware wannan matsala, amma ba ƙarfin soji ba”, in Sanata Kawu Sumaila.
Ya ƙara da cewa ƙungiyarsu tana la’akari da kusancin Nijar da Arewacin Najeriya
“‘jihohin Najeriya kusan guda bakwai duk sun yi iyaka da Nijar kuma kusan duka waɗannan jihohi, akwai matsalolin tsaro, kama daga na Boko-Haram zuwa na ‘yan fashin daji”.
”Idan muka bari aka fara yaƙi tsakanin Najeriya da Nijar to masifar da Najeriya za ta shiga, ita kanta Nijar dinma ba za ta shiga wanna masifa ba”, in ji Sanatan da ke wakilar Kano ta Kudu.
Sanata Kawu Sumaila ya ce hakan zai sa ‘yan ta’addan take waɗannan yankuna su ƙara samun dama wajen ci gaba da ɓarnar da suke gudanarwa.
Ya ƙara da cewa ”kuma yanzu halin da talakawan ƙasar nan ke ciki na matsin rayuwa da sauran matsaloli, idan aka fara yaƙin gaskiya yankunan Najeriya da ke iyaka da Nijar za su sake shiga cikin wata masifa”.
A ranar Juma’a ne shugaban Najeriya Bola Tinubu, kuma shugaban Ecowas, ya aike wa Majalisar Dattawan Najeriya buƙatar amincewarta domin tura sojojin ƙasar zuwa Jamhuriyar Nijar.