fidelitybank

Ba mu san dalilin da ya sa za a yi zanga-zanga ba – Gwamnonin APC

Date:

Ƙungiyar Gwamnonin Jam’iyyar APC ta ce, ba ta san dalilin da ya sa wasu ‘yan Najeriya ke shirin gudanar da zanga-zanga ba.

Yayin da yake jawabi a taron manema labarai jim kaɗan bayan kammala taron ƙungiyar a Abuja, babban birnin ƙasar, shugaban ƙungiyar – wanda shi ne gwamnan jihar Imo, Hope Udozinma – ya ce ”mu ba mu san dalilin da ya sa suke shirin yin zanga-zangar ba, inda mun sani za mu gayyace su don zama da su domin samun maslaha”.

“Mu a matsayinmu na jagorori muradinmu shi ne haɗin kan ƙasar nan, muna maraba da duk wani abu da zai kawo wa ƙasarmu da al’umarmu ci gaba ta hanyar samar da ayyukan yi ga matasa maza da mata da ke kammala karatu”, in ji shugaban gwamnonin na APC.

Uzodinma ya ƙara da cewa rashin wayewa ne a ce za a shirya zanga-zanga a Najeriya a wannan hali da ake ciki, yana mai kira ga ‘yan ƙasar da su kaurace wa yunƙurin zanga-zangar.

Gwamnan ya kuma yi kira ga ‘yan Najeriya su yi wa gwamnati haƙuri, yana mai cewa gwamnati na iya bakin ƙoƙarinta don magance matsin tattalin arzikin da ƙasar ke fama da shi.

daily post nigeria today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp