Ƙungiyar Fulani makiyaya ta ‘Mi Yetti Allah’ (MACBAN) tace babu wani dan takar da ta nunawa goyon baya da yake neman shugabancin Najeriya, haka zalika ba ta nuna goyon baya ga wata jam’iyyar siyasa ba gme da zaben da ke tafe na 2023.
Shugaban kungiyar na kasa Alhaji Baba Usman-Ngelzarma ne ya bayyana hakan yayin da yake tattaunawa da manema labarai a Abuja a ranar Juma’a, yana cewa duka manyan jam’iyyun siyasar ba su sanyan manyan kalubalen da Najeriya ke fuskanta ba cikin manufofinsu.
Ya kara da cewa ” ya kamata na bayyana komi a bude muna da kungiyar Miyetti Allah biyu. Muna da Miyetti Allah Kautal Hore da kuma Miyetti Allah (MACBAN) wadda nake shugabanta a mataki na kasa.
“Dan gane da kungiyata, ba mu ayyana wani dan takarar shugabn kasa da muke goyon baya ba ya zuwa yanzu.”