Kungiyar ‘yan awaren yankin kudu maso gabas mai fafutukar kafa kasar Biafra (IPOB), ta musanta zargin da rundunar sojin Najeriya ta yi na cewa, ita ce ke da alhakin kisan gillar da aka yi wa wasu sojoji a jihar Imo.
A ranar Talata ne rundunar sojin Najeriya ta zargi kungiyar IPOB da kuma kungiyar tsaro ta Eastern Security Network (ESN), da laifin kashe wasu jami’anta guda biyu, Master Warrant Officer (MWO) Audu M Linus (mai ritaya) da kuma Private (Pte) Gloria Matthew.
Marigayin, a cewar daraktan hulda da jama’a na rundunar, Birgediya Janar Onyema Nwachukwu, ya gamu da ajalin su ne a ranar Asabar, 30 ga Afrilu, 2022, a lokacin da suke kan hanyar zuwa jihar Imo domin bikin aurensu na gargajiya.
Sai dai a martanin da ta mayar kan wannan zargi, kungiyar ta IPOB a wata sanarwa da ta fitar a ranar Larabar da ta gabata ta hannun mai magana da yawunta, Emma Powerful, ta nesanta mambobinta da hannu a zargin kisan sojojin biyu.