fidelitybank

Ba mu kama Dan Jaridar da ya yi hira da abokan hamayya ba – Gombe

Date:

Gwamnatin jihar Gombe ta musanta bayar da umarnin kama wani dan jarida a gidan rediyo, saboda karbar bakuncin wani dan jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP) kamar yadda jam’iyyar ta yi zargin.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Alhaji Shuaibu Gara, mai ba Gwamna Inuwa Yahaya shawara na musamman kan harkokin yada labarai da dabaru kuma ya bayyanawa manema labarai a Gombe ranar Lahadi.

Kamfanin Dillancin Labarai na kasa, NAN, ta tuna cewa, wani dan jarida da ke aiki da Jewel FM Gombe, tare da bakon sa, ‘yan sanda sun kama shi tare da tsare shi bayan shirya wani shiri.

“Abin da muka sani shi ne gwamnati ta kai karar ‘yan sanda cewa, mun sanya ido a kan wani shiri na mintuna 30 na rediyo inda aka gayyaci bako zuwa shirin siyasa.

“Kuma a cikin shirin, bakon ya yi zargin cewa gwamnati ta kashe Naira biliyan 4 don katangar gidan gwamnati.

“Mun gabatar wa ‘yan sanda bayanan mu na kasafin kudin jihar baki daya don kula da duk wasu gine-ginen gwamnati tsakanin 2019 zuwa 2022. Don mu yi masa adalci mu ma muna son ‘yan sanda su nemi ya ba shi shaidarsa.

“Ta yaya wani zai ce mun kashe sama da Naira biliyan 4 don kawai katangar gidan gwamnati kadai.

“Idan aka fuskanci masu bincike, wanda ake zargin bai ma san adadin miliyan nawa ya kai Naira biliyan 1 ba,” in ji shi.

Ya kuma kalubalanci ‘yan adawa da su bayar da hujjar cewa an kama duk wani dan jarida, inda ya kara da cewa gwamnati kawai ta gabatar da kara ga ‘yan sanda a kan bakon gidan rediyon da ya yi zargin rashin gaskiya a kan gwamnati.

“Gwamnatin Gombe ba ta bayar da umarnin kama wani dan jarida ba, duk wanda ya ce an kama dan jarida, to dan jaridan ya nuna mana amincewar kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya (NUJ),” inji shi.

Gara ya kuma yi kira ga jama’a masu son samun duk wani bayani daga gwamnati da su bi hanyoyin da suka dace.

leadership news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...
X whatsapp