fidelitybank

Ba mu kama Dan Jaridar da ya yi hira da abokan hamayya ba – Gombe

Date:

Gwamnatin jihar Gombe ta musanta bayar da umarnin kama wani dan jarida a gidan rediyo, saboda karbar bakuncin wani dan jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP) kamar yadda jam’iyyar ta yi zargin.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Alhaji Shuaibu Gara, mai ba Gwamna Inuwa Yahaya shawara na musamman kan harkokin yada labarai da dabaru kuma ya bayyanawa manema labarai a Gombe ranar Lahadi.

Kamfanin Dillancin Labarai na kasa, NAN, ta tuna cewa, wani dan jarida da ke aiki da Jewel FM Gombe, tare da bakon sa, ‘yan sanda sun kama shi tare da tsare shi bayan shirya wani shiri.

“Abin da muka sani shi ne gwamnati ta kai karar ‘yan sanda cewa, mun sanya ido a kan wani shiri na mintuna 30 na rediyo inda aka gayyaci bako zuwa shirin siyasa.

“Kuma a cikin shirin, bakon ya yi zargin cewa gwamnati ta kashe Naira biliyan 4 don katangar gidan gwamnati.

“Mun gabatar wa ‘yan sanda bayanan mu na kasafin kudin jihar baki daya don kula da duk wasu gine-ginen gwamnati tsakanin 2019 zuwa 2022. Don mu yi masa adalci mu ma muna son ‘yan sanda su nemi ya ba shi shaidarsa.

“Ta yaya wani zai ce mun kashe sama da Naira biliyan 4 don kawai katangar gidan gwamnati kadai.

“Idan aka fuskanci masu bincike, wanda ake zargin bai ma san adadin miliyan nawa ya kai Naira biliyan 1 ba,” in ji shi.

Ya kuma kalubalanci ‘yan adawa da su bayar da hujjar cewa an kama duk wani dan jarida, inda ya kara da cewa gwamnati kawai ta gabatar da kara ga ‘yan sanda a kan bakon gidan rediyon da ya yi zargin rashin gaskiya a kan gwamnati.

“Gwamnatin Gombe ba ta bayar da umarnin kama wani dan jarida ba, duk wanda ya ce an kama dan jarida, to dan jaridan ya nuna mana amincewar kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya (NUJ),” inji shi.

Gara ya kuma yi kira ga jama’a masu son samun duk wani bayani daga gwamnati da su bi hanyoyin da suka dace.

opra news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...
X whatsapp