Ƙungiyar ci gaban yankin Neja Delta PANDEF, ta nuna rashin jin daɗinta kan hukuncin kotun ƙoli, wadda ta umarci babban akanta da babban bankin Najeriya su dakatar da ba jihar Rivers kasonta na tarayya.
Sakataren watsa labarai na ƙungiyar, Chief Obiuwevbi Ominimini ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a madadin ƙungiyar, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.
“Mutanen jihar, waɗanda ba su aikata laifin komai ne za su shiga matsala. Kuma ganin yadda jihar Rivers take kan gaba wajen tara wa ƙasar kuɗin shiga ta fannin man fetur da iskar gas, jihar ba ta cancanci shiga tasku ba saboda saɓanin siyasa.”
“Lallai hana jihar kasonta zai jefa ƴan jihar cikin ƙunci da damuwa,” in ji sanarwa, inda ta ƙara da cewa a shirye ƙungiyar take wajen tabbatar da sulhu da haɗin kai a yankin na Neja Delta.