fidelitybank

Ba mu ga dalilin sauya matsayinmu ba akan shiyya-shiyya – PDP

Date:

Gwamnonin jam’iyyar PDP na Kudancin Najeriya sun dage cewa, ya kamata jam’iyyar ta tsayar da tikitin takarar shugaban kasa a 2023 zuwa yankin kudanci, domin yin gaskiya da adalci.

Gwamnonin jam’iyyar adawa, sun bayyana matsayarsu kan batun shiyya-shiyya yayin da suke zantawa da manema labarai bayan ganawar da suka yi a daren Juma’a a masaukin Gwamnan Akwa-Ibom, Asokoro, Abuja.

Gwamnan jihar Abia, Dr Okezie Ikpeazu, wanda ya yi magana a madadin gwamnonin, ya ce, sun sa ido sosai kan abubuwan da ke faruwa a jam’iyyar PDP dangane da shiyya-shiyya, amma ba su da dalilin sauya matsayarsu a baya.

“Matsayinmu shi ne na farko, mun jajirce wajen hadin kan jam’iyyarmu, kuma mun yi aiki tukuru don ganin cewa, jam’iyyar ta ci gaba da kasancewa mai karfi da kuma abin dogaro don ‘ceto’ Najeriya a 2023.

“Ko ma dai, muna so mu ja hankalin ku kan yadda muka amince a matsayinmu na gwamnonin Kudancin Legas da kuma a Delta cewa jam’iyyar ta mutunta ka’idar shiyya-shiyya kamar yadda kundin tsarin mulkinmu ya tanada.

“Saboda haka, muna jin cewa abin da ya fi dacewa a yi shi ne shiyyar shugabancin kasa zuwa Kudu, kuma mun tsaya kan wannan matsayi.

“Ba mu ga dalilin sauya matsayinmu ba, domin an kafa jam’iyyar ne bisa adalci da gaskiya.

“Muna kuma tunanin cewa, adalci da gaskiya sune ginshiƙai masu mahimmanci waɗanda za su daidaita siyasarmu zuwa tafiyarmu na ceto Najeriya,” in ji Ikpeazu.

ng news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...
X whatsapp