Gwamnonin jam’iyyar PDP na Kudancin Najeriya sun dage cewa, ya kamata jam’iyyar ta tsayar da tikitin takarar shugaban kasa a 2023 zuwa yankin kudanci, domin yin gaskiya da adalci.
Gwamnonin jam’iyyar adawa, sun bayyana matsayarsu kan batun shiyya-shiyya yayin da suke zantawa da manema labarai bayan ganawar da suka yi a daren Juma’a a masaukin Gwamnan Akwa-Ibom, Asokoro, Abuja.
Gwamnan jihar Abia, Dr Okezie Ikpeazu, wanda ya yi magana a madadin gwamnonin, ya ce, sun sa ido sosai kan abubuwan da ke faruwa a jam’iyyar PDP dangane da shiyya-shiyya, amma ba su da dalilin sauya matsayarsu a baya.
“Matsayinmu shi ne na farko, mun jajirce wajen hadin kan jam’iyyarmu, kuma mun yi aiki tukuru don ganin cewa, jam’iyyar ta ci gaba da kasancewa mai karfi da kuma abin dogaro don ‘ceto’ Najeriya a 2023.
“Ko ma dai, muna so mu ja hankalin ku kan yadda muka amince a matsayinmu na gwamnonin Kudancin Legas da kuma a Delta cewa jam’iyyar ta mutunta ka’idar shiyya-shiyya kamar yadda kundin tsarin mulkinmu ya tanada.
“Saboda haka, muna jin cewa abin da ya fi dacewa a yi shi ne shiyyar shugabancin kasa zuwa Kudu, kuma mun tsaya kan wannan matsayi.
“Ba mu ga dalilin sauya matsayinmu ba, domin an kafa jam’iyyar ne bisa adalci da gaskiya.
“Muna kuma tunanin cewa, adalci da gaskiya sune ginshiƙai masu mahimmanci waɗanda za su daidaita siyasarmu zuwa tafiyarmu na ceto Najeriya,” in ji Ikpeazu.