Hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) reshen jihar Ondo, ta yi watsi da rahoton da ke cewa jamiāanta sun daki mata a ciki a kan babbar hanyar Akure ranar Asabar.
Kwamandan hukumar ta FRSC reshen jihar, Ezekiel SonAllah wanda ya yi watsi da ikirarin a cikin wata sanarwa ya ce, rahoton da aka yada a shafin Twitter ya yi zargin cewa, matar ta zubar da jini bayan da wani jamiāin ya dake ta a ranar Asabar a kan babbar hanyar Akure.
Kwamandan sashin ya ce, ba a yi wa matar duka ba kamar yadda ake ikirari.
Ya ce motar da take ciki ta tsaya ne kawai a lokacin da direban ya ki bin umarnin tsayawa, sannan ya yi yunkurin bi ta kan wasu sojoji biyu.
SonAllah ya yi ikirarin cewa motar ta yi kofin wuce Ęima, kuma direban bai yi amfani da bel din ba.
Ya ce motocin biyu sun taho ne daga keji a Osun suna zuwa Ogbese a karamar hukumar Akure ta Arewa a jihar Ondo lokacin da jamiāan hukumar FRSC suka tare su.
Kwamandan sashin ya yi zargin cewa motar ta biyu ita ma ba ta so tsayawa sai direban ya fuskanci Marshal Aboluja da motar a yunkurinsa na tserewa.
Ya kuma yi zargin cewa direban ya kuma yi yunkurin kutsawa kan wani Marshal, Olamogoke, kafin daga bisani motar ta tsaya tare da taimakon sauran āyan tawagar.
“Nan da nan sai motar ta tsayar da fasinjojin suka fito suka fara kuka, da isar su sai wata mata ta yi zargin cewa an buge ta, amma babu wani abu da ya shafi matar, ba jini.”
Ya ce lokacin da matar ta dage cewa tana jin zafi, sai jamiāan tsaro suka kai ta wani asibiti da ke kusa.