Gwamnatin Amurka, ta ce, ba ta da zabi tsakanin ‘yan takarar da za su fafata a zaben 2023.
Gwamnatin Amurka ta kuma ce, ba ta da wata jam’iyyar siyasa da ta fi so ya lashe zaben 2023 a Najeriya.
Will Stevens, karamin jakada na Ofishin Jakadancin Amurka a Legas, ya ce, ya na da sha’awar tabbatar da buri na ‘yan Najeriya ya tabbata, wanda ya kasance sahihi, gaskiya, da kuma zabe cikin lumana.
Stevens ya bayyana hakan ne a taron ranar yaki da cin hanci da rashawa ta kasa da kasa wanda karamin ofishin tare da hadin gwiwar BudgIT suka shirya a karshen mako.
A cewar Stevens: “Idan muka mai da hankali kan zabukan da ke tafe a Najeriya, bari in bayyana a fili cewa, Amurka ba ta da wani dan takara ko jam’iyya da ta fi so a zabe mai zuwa.
“Sha’awarmu ita ce tallafawa sahihin zabe, gaskiya, kuma cikin lumana da zai wakilci muradin ‘yan Najeriya.
“Mun bukaci dukkan ‘yan Najeriya da su yi watsi da amfani da tashin hankali da kalamai masu tayar da hankali a lokacin da kuma bayan ranar zabe.”