fidelitybank

Ba mu da niyyar ƙara farashin litar mai – NNPCL

Date:

Kamfanin samar da man fetur na NNPCL, ya bai wa masu sayen mai a gidajen man fetur dinsa cewa ba shi da niyyar kara kudin litar mai.

A cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na X tsohon shafin Tuwita, NNPC ya ce sabanin rade-radin da ake yi na karin farashin litar mai a kasar, masu sayen man fetur na iya ci gaba da shan mai a gidan man fetur dinsa da ke fadin kasar a cikin farashin mafi rahusa.

Sanarwar NNPC na zuwa daidai lokacin da wasu kafofin yada labaran Najeriya ke cewa farashin litar mai a tashoshin sauke man fetur na kasar, ya kai naira 720 duk lita daya, abin da ya sa ake jin farashin zai iya kai wa naira 729 a gidajen mai matukar gwamnatin kasar ba ta ci gaba da biyan kudin tallafi ba.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa harkoki sun tsaya a tashoshin sauke man fetur, yayin da a wasu wurare, wasu gidajen man fetur suka rufe.

Wasu direbobin mota a birane kamar Abuja da Kano sun ba da rahotannin cewa sun sha mai a farashin da ya haura abin da aka saba sayarwa a baya.

natforce 
latest news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp