Tsohon shugaban ƙasa, Goodluck Jonathan, ya yi watsi da fom din tsayawa takarar shugaban kasa da aka siya ma sa ba tare da tuntubarsa ba.
A ranar Litinin 9 ga watan Mayun 2022 ne wata kungiya mai suna “Fulani Group” ta sayawa tsohon shugaban fom din takarar a karkashin jam’iyyar APC mai mulki wadda ta kada shi a zaben da aka yi a shekarar 2015, bayan shafe shekaru biyar ya na mulkin kasar.
Ƙungiyar magoya bayan Jonathan din ce ta yi karo-karo tare da saya wa tsohon shugaban fom din.
Sai dai sanarwar da mai magana da yawun Mista Jonathan ya fitar, ya ce ”ba mu da masaniya, ba kuma a tuntube mu ba kafin yanke hukuncin sayan fom din.”