fidelitybank

Ba mu da hannu a rikicin masarautar Kano – Sojoji

Date:

Rundunar sojin kasar nan ta musanta cewa tana da hannu a rikicin masarautu da ke faruwa a jihar Kano.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun daraktan hulda da jama’a na rundunar, Manjo-Janar Onyema Nwachukwu a ranar Lahadin da rundunar ta wallafa a shafin sada zumuntarta naX.

A ranar Alhamis ɗin da ta gabata ne wata babbar kotun tarayya da ke Kano ta bayar da umurnin hana Gwamna Abba Yusuf mayar da Sarki Muhammadu Sanusi II kan karagar mulki.

Kotun ta kuma dakatar da aiwatar da sabuwar dokar da ta soke masarautun Bichi da Gaya da Karaye da kuma Rano.

Duk da umarnin kotun, gwamnan jihar, Abba Yusuf, ya mayar da Sanusi a matsayin sarkin Kano, yana mai cewa “alkalin da ya bayar da wannan umarni ba ya cikin Najeriya a lokacin ba ya bayar da umarnin”.

“Saɓanin ra’ayin kungiyar lauyoyin Najeriya reshen jihar Kano kamar yadda jaridar Premium Times ta buga a ranar 26 ga Mayu 2024, sojojin Najeriya ba su da hannu a rikicin masarautar Kano kuma ba su da hannu wajen aiwatar da wani umarnin kotu. Sun dauki matakin ne kawai don duba duk wata matsala ko zagon kasa da za a iya samu a rikicin masarautar Kano.” in ji sanarwar.

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Batun da ya fi ɗaukar hankalin sojojin Najeriya da sauran jami’an tsaro shi ne hana tabarbarewar doka da oda a jihar”

Rundunar sojin ta ce za ta shiga tsakani ba tare da ɓata lokaci ba idan aikin tabbatar da tsaro na neman ya fi ƙarfin ‘yan sanda.

“Duk abin da Sojoji ke yi a wannan mataki shi ne sanya ido kan lamarin da kuma kasancewa cikin shirin ko-ta-kwana idan lamarin ya ta’azzara da zai kawo barazana ga tsaron jihar da ma yankin baki daya.” in ji sanarwar.

An sake nada Sanusi a matsayin Sarkin Kano na 14 bayan sauke shi daga karagar mulki da tsohuwar gwamnatin jihar ta yi.

Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya amince da sake nada shi a makon da ya gabata, bayan amincewa da kudurin dokar masarautar jihar Kano na 2024 wanda aka gyara da majalisar ta amince a kai.

Tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Ganduje dai ya sauke Sanusi daga muƙaminsa a ranar 9 ga Maris, 2020 bayan zargin sa da almundahana da kuɗain masarauta da kuma rashin biyayya.

the punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp