fidelitybank

Ba mu amince da dubu 70 ba a matsayin sabon albashi – NLC

Date:

Ƙungiyar ƙwadago ta TUC a Najeriya ta yi watsi da ƙarin albashin da gwamnatin tarayyar ƙasar ta sanar a ranar Talata, kwana ɗaya gabanin bikin ranar ma’aikata ta duniya.

A jiya ne wata sanarwa wadda ta samu sa hannun shugaban hukumar kula da albashin ma’aikata ta Najeriya, Ekpo Nta, ta bayyana cewa an yi ƙarin kashi 25 zuwa 35 cikin ɗari a kan albashin ma’aikatan gwamnati.

Hakan ya nuna cewa mafi ƙarancin albashi zai koma kimanin naira 37,000 daga naira 30,000 da ake da shi a baya.

Sai dai a tattaunawar sa da BBC, sakataren ƙungiyar ƙwadago ta TUC, kwamared Nuhu Abbayo Toro ya ce ba da sanin ƙungiyoyin ƙwadago aka yi ƙarin albashin ba kuma ba su amince da shi ba.

Toro ya ce “abin da dokar ƙasa ta ce shi ne sai an zauna an tattauna an yi yarjejeniya an samu matsaya kafin a amince da albashi mafi ƙanƙanta”.

Ya ƙara da cewa “ba daidai ba ne shugaban ƙasa ya furta cewa ya yi ƙarin albashin ma’aikata alhali akwai kwamitin da ke aikin samar da sabon albashi mafi ƙaranci”.

Shi ma shugaban ƙungiyar ƙwadago ta NLC, Joe Ajaero a wata tattaunawa da kafar talabijin ta Channels da safiyar Talata ya ce “sanarwar da aka bayar an yi ta ne da wata manufa domin kuwa babu wani ƙarin albashi da aka yi”.

A watan Janairu ne Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta ƙaddamar da wani kwamiti wanda zai duba tare da yanke shawara kan ƙarancin albashin ma’aikata a ƙasar.

An ɗauki matakin ne bayan barazanar da ƙungiyoyin ƙwadago na ƙasar suka yi kan cewa za su tsayar da lamurra cak a ƙasar har sai gwamnatin tarayya ta samo mafita game da matsin rayuwa da ma’aikatan ƙasar ke fuskanta.

Al’ummar Najeriya na fuskantar tashin farashin kayan masarufi tun bayan da shugaban ƙasar ya sanar da janye tallafin man fetur da gwamnati ke bayarwa a ranar 29 ga watan Mayun 2023.

spw

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp