fidelitybank

Ba ma goyon bayan tsige Sarakunan Kano – Ƙungiya

Date:

Wata kungiya mai suna Inuwar Masarautun Kano Biyar (IMAK) ta yi kira ga majalisar dokokin jihar Kano da ta yi watsi da rokon wata kungiya mai suna ‘Yan Dagwalen Kano – wadda a baya-bayan nan ta bukaci a rusa masarautun jihar guda hudu tare da mayar da tsohon sarki Khalipha Sanusi Lamido Sanusi.

Kiran na kunshe cikin wata sanarwa da shugaban kungiyar ta IMAK, Nasiru Ibrahim Rano ya aike wa shugaban majalisar dokokin jihar Kano.

Kungiyar ta IMAK ta ce rushe masarautun kamar mayar da hannun agogo baya ne duba da rawar da suke takawa wajen samar da ci gaba ga al’ummarsu.

Sanarwar ta bayyana illar rushe masarautun da ta ce yin hakan ka iya rikidewa zuwa matsalar tsaro da za ta jefa rayuka da dukiyoyin jama’a cikin wani hali.

A cewarta, kyale masarautun zai ba da dama wajen farfado da martabarsu wanda hakan hanya ce da za ta taimaka wajen gaggauta aiwatar da manufofin gwamnati.

Ta kara da cewa ana girmama duka sarakunan inda sanarwar ta ce a shirye suke su yi iya karfinsu domin tabbatar da zaman lafiya da bunkasar tattalin arziki a jihar Kano.

“Babu wani sarki da aka taba samu da hannu a cin hanci da rashin da’a ko yin ba daidai ba, a don haka kyale su a kan mukamansu shi ne abu mafi dacewa a wannan lokaci.” kamar yadda sanarwar kungiyar ta bayyana.

A karshe kungiyar ta yi kira ga majalisar dokokin da ta saurari bukatarsu ta kuma duba kiran saboda zaman lafiya a Kano.

legit nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp