fidelitybank

Ba ma goyon bayan tsige Sarakunan Kano – Ƙungiya

Date:

Wata kungiya mai suna Inuwar Masarautun Kano Biyar (IMAK) ta yi kira ga majalisar dokokin jihar Kano da ta yi watsi da rokon wata kungiya mai suna ‘Yan Dagwalen Kano – wadda a baya-bayan nan ta bukaci a rusa masarautun jihar guda hudu tare da mayar da tsohon sarki Khalipha Sanusi Lamido Sanusi.

Kiran na kunshe cikin wata sanarwa da shugaban kungiyar ta IMAK, Nasiru Ibrahim Rano ya aike wa shugaban majalisar dokokin jihar Kano.

Kungiyar ta IMAK ta ce rushe masarautun kamar mayar da hannun agogo baya ne duba da rawar da suke takawa wajen samar da ci gaba ga al’ummarsu.

Sanarwar ta bayyana illar rushe masarautun da ta ce yin hakan ka iya rikidewa zuwa matsalar tsaro da za ta jefa rayuka da dukiyoyin jama’a cikin wani hali.

A cewarta, kyale masarautun zai ba da dama wajen farfado da martabarsu wanda hakan hanya ce da za ta taimaka wajen gaggauta aiwatar da manufofin gwamnati.

Ta kara da cewa ana girmama duka sarakunan inda sanarwar ta ce a shirye suke su yi iya karfinsu domin tabbatar da zaman lafiya da bunkasar tattalin arziki a jihar Kano.

“Babu wani sarki da aka taba samu da hannu a cin hanci da rashin da’a ko yin ba daidai ba, a don haka kyale su a kan mukamansu shi ne abu mafi dacewa a wannan lokaci.” kamar yadda sanarwar kungiyar ta bayyana.

A karshe kungiyar ta yi kira ga majalisar dokokin da ta saurari bukatarsu ta kuma duba kiran saboda zaman lafiya a Kano.

today nation

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp