Jakadar Amurka a Najeriya, Mary Leonard, a ranar Laraba, ta sake nanata goyon bayan kasarta ga gudanar da zabe mai sahihanci da zai bayyana aniyar ‘yan Najeriya.
Ta sanar cewa Amurka ba za ta goyi bayan wani dan takara ba a zaben da ke tafe.
Wannan jawabin na zuwa ne kwana 24 gabanin zaben shugaban kasar da jam’iyyu 18 za su fafata akai.
Ta kuma sake yin gargadi cewa Amurka za ta kakaba takunkumin hana shiga kasarta ga dukkan wadanda aka samu da hannu wajen yi wa zaben kafar ungulu.
“A shekarun baya mun dauki matakan saka wa wasu takunkumi bayan da muka gano cewa sun yi katsalandan a zabukan Najeriya. Sannan sakataren harkokin waje na Amurka Anthony Blinken a mako jiya ya sanar cewa za mu dauki matakan ladabtarwa kan dukkan wadanda ke yin haka.”