Wakilin Amurka a Majalisar Dinkin Duniya, Robert Wood, ya ce ba za su goyi bayan tsagaita buɗe wuta a Gaza nan take ba.
“Yayin da Amurka ke matuƙar goyon bayan zaman lafiya mai dorewa, wanda Isra’ilawa da Falasdinawa za su iya rayuwa cikin lumana da tsaro, ba ma goyon bayan kiran tsagaita buɗe wuta a Gaza cikin gaggawa.”
“Wannan zai yi shuka gabar da za ta haifar da yaƙi na gaba saboda Hamas ba ta da sha’awar ganin dorewar zaman lafiya,” kamar yadda ya shaida wa kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya.
Amurka tana ɗaya daga cikin membobin dindindin waɗanda ke da haƙƙin yin watsi da ƙudurin.