fidelitybank

Ba ma cikin ƙasashen da Saudiyya ta daina bai wa biza – Gwamnatin Tarayya

Date:

Ma’aikatar Harkokin Waje ta Najeriya ta musanta cewa ƙasar na cikin jerin ƙasashe da Saudiyya ta hana ba su biza daga 13 ga watan Afrilu.

Kamfanin labarai na Najeriya NAN ya ruwaito Ministan Harkokin Waje Yusuf Maitama Tuggar na yin ƙarin bayanin ta bakin mataimakinsa na musamman kan kafofin yaɗa labarai, Alkasim Abdulkadir, ranar Litinin.

Ministan ya ce Saudiyya ta tabbatar musu cewa jerin sunayen da ke nuna Najeriya na cikinsu, wanda kuma aka dinga yaɗawa a shafukan sada zumunta, ba na gaskiya ba ne.

“Hukumar Saudiyya ta tabbatar babu wani umarni mai kama da haka, dokokin da aka saka a hyanzu sun shafi aikin Hajji ne kawai. A gane cewa, dokokin sun shafi masu bizar yawon buɗe ido ne kawai a lokacin aikin Hajji,” a cewarsa.

Bisa ƙa’idojin, an haramta wa masu bizar yawon buɗe ido yin aikin Hajji, ko shiga Makkah tun daga 29 ga watan Afrilu zuwa 11 ga Yuni (ko kuma 1 ga watan Zul Ƙida zuwa 14 ga Zul Hijjah na kalandar Musulunci).

Jerin sunayen da aka dinga yaɗawar na ƙunshe da ƙasashen Masar, Pakistan, Indiya, da kuma Najeriya.

national tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp