Hukumar yaki da masu aikata miyagun laifuka a Birtaniya ta ce, wasiku biyu da suka zargi ‘yan takarar mukamin shugaban kasa a Najeriya da jam’iyyun siyasar kasar da aikata ba dai-dai ba, wadanda aka rika yadawa a shafukan sada zumunta na jabu ne.
Dubban mutane ne sun karanta wasikun da aka wallafa a Twitter da ake zargin hukumar ta NCA ce ta wallafa su.
Karanta Wannan:Â Yankin Kudu maso Yamma ne zai gaji Buhari – Tinubu
Wasika ta farko da ta bayyana a karshen watan da ya gabata amsa ce ta bogi ga wani bincike da ake yi kan zargin da ake yi wa dan takarar shugaban kasa na jamiyyar APC mai mulkin kasar Bola Ahmed Tinubu da almundahana.
Ita kuwa wasika ta biyu ta yi ikirarin cewa hukumar ta NCA na binciken jam’iyyar hammaya ta Labour kan zargin rubuta wasikar ta farko ta bogi.