fidelitybank

Ba gudu ba ja da baya sai mun gudanar da zabe – Adeleke

Date:

Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke ya ce, babu gudu babu ja da baya kan zaɓen ƙananan hukumomin da za a yi a jihar a gobe Asabar.

Gwamnan ya yi wannan jawabin ne a matsayin martani kan shawarar da ministan shari’a na Najeriya, Lateef Fagbemi, wanda ya buƙaci gwamnatin jihar ta dakatar da yunƙurinta na shirya sabon zaɓen na ƙananan hukumomi.

Ministan ya ce zaɓaɓɓun shugabannin ƙananan hukumomin da gwamnan ya gada – waɗanda ƴan jam’iyyar APC ne shi kuma ɗan PDP- wa’adinsu bai ƙare ba, don haka bai kamata a cire su ba, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

A wata sanarwa da kakakin gwamnan, Olawale Rashed ya fitar, Adeleke, ya ce sun shirya tsaf, kuma babu gudu babu ja da baya kan gudanar da zaɓen.

“Ina kira ga dukkan masu ruwa da tsaki daga ciki da wajen jihar da su yi biyayya ga tsare-tsaren dimokuraɗiyya. Mu dai muna amfani da doka da oda ne. Don haka za a yi zaɓe, kuma ina kira ga dukkan ƴan jihar da su gudanar da zaɓen cikin lumana, domin Osun jiha ce da aka santa da zaman lafiya.”

bbc news nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp