Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke ya ce, babu gudu babu ja da baya kan zaɓen ƙananan hukumomin da za a yi a jihar a gobe Asabar.
Gwamnan ya yi wannan jawabin ne a matsayin martani kan shawarar da ministan shari’a na Najeriya, Lateef Fagbemi, wanda ya buƙaci gwamnatin jihar ta dakatar da yunƙurinta na shirya sabon zaɓen na ƙananan hukumomi.
Ministan ya ce zaɓaɓɓun shugabannin ƙananan hukumomin da gwamnan ya gada – waɗanda ƴan jam’iyyar APC ne shi kuma ɗan PDP- wa’adinsu bai ƙare ba, don haka bai kamata a cire su ba, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.
A wata sanarwa da kakakin gwamnan, Olawale Rashed ya fitar, Adeleke, ya ce sun shirya tsaf, kuma babu gudu babu ja da baya kan gudanar da zaɓen.
“Ina kira ga dukkan masu ruwa da tsaki daga ciki da wajen jihar da su yi biyayya ga tsare-tsaren dimokuraɗiyya. Mu dai muna amfani da doka da oda ne. Don haka za a yi zaɓe, kuma ina kira ga dukkan ƴan jihar da su gudanar da zaɓen cikin lumana, domin Osun jiha ce da aka santa da zaman lafiya.”