Kungiyar malaman jami’o’i ta kasa (ASUU) ta ce nan ba da dadewa ba za ta shiga yajin aikin sai baba-ta-gani, domin biyan bukatunsu sama da shekara guda bayan ta dakatar da yajin aikin na watanni tara.
Kamfanin dilancin labarai na kasa NAN, ya rawaito cewa, shugaban kungiyar reshen jami’ar Jos (UNIJOS), Lazarus Maigoro ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis a garin Jos.
Kungiyar ta dakatar da yajin aikin na tsawon watanni tara a watan Disamba 2020, bayan ta koka da gazawar gwamnatin tarayya wajen magance duk wasu batutuwan da suka taso a cikin yarjejeniyar 2009 da ta shiga da kungiyar.
Maigoro, wanda ya bayyana gwamnatin tarayya a matsayin “gwamnati mara ainganci” ya ce, kungiyar ba za ta yi kasa a gwiwa ba, har sai an daukaka darajar ilimi a kasar nan.