Gwamnatin jihar Bauchi, ta yi ƙarin haske kan dalilin da ya sa aka cire Wazirin Bauchi, Alhaji Bello Kirfi daga mukaminsa na Waziri.
Gwamnatin ta ce, tsohon Wazirin ba ya kama girmansa ne a wuraren da hukuma ba za ta iya zuba masa ido ba.
A ranar Larabar da ta wuce ne fadar jihar Bauchin ta sanar da tuɓe rawanin Wazirin.
Sai dai bangaren Wazirin ya yi zargin cewa, gwamnan jihar ne ya saka masa karan-tsana, saboda yana goyon bayan dan takarar shugaban ƙasa na jam`iyyar PDP, Atiku Abubakar.
Atiku kar ka shirya da Wike duk wanda ya tsayar ba nasara – Eze
Hon Abdurrazak Nuhu Zaki, kwamishinan ƙananan hukumomi da masarautun gargajiya na jihar ya shaida wa BBC cewa, matakin da aka ɗauka sam ba shi da alaƙa da Atiku Abubakar, hasalima, a cewarsa, masu danganta lamarin da ɗan takarar, ƙarya suke.
Ya ce “umarnin da gwamnan jihar Bauchi ya bayar tun da aka fara kamfe, ga duk wani ɗan Jam’iyyar PDP, ya yi tallan Atiku Abubakar, ya kuma yi tallan gwamna,”
Ya ƙara da cewa Gwamnan jihar Bauchi ya kafa kwamiti na tallan ƴan takarar Jam;’iyyar PDP daga sama har ƙasa, “don haka wani ya zo ya ce wai Alhaji Muhammadu Bello Kirfi ya rasa kujerarsa wai saboda taron a tallata Atiku Abubakar, ya yi ƙarya kuma ya yaudari kansa.”